ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihohi Sun Kashe Naira Biliyan 139.92 Wajen Biyan Bashin Kasashen Ketare A Wata 6

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
2 years ago
Bashi

Jihohin Nijeriya sun kashe naira biliyan 139.92 daga cikin kudaden da suka karba a wurin gwamnatin tarayya a watanni 6 na farkon shekarar 2024.

 

Wannan bayanai dai yana kunshe a cikin kididdigan da kwamitin asusun rarraba kudade ta tarayya wacce ta samu daga bayanan hukumuar kididdiga ta kasa (NBS).
Kudaden da aka kashe ya kkaru da kashi 122% daga naira biliyan 63.06 da aka kashe a shekarar da ta gabata na watanni shidar farkon shekara.

ADVERTISEMENT
  • Yadda Mutane Ke Tona Ramin Tururuwa Don Neman Abinci A Borno
  • An Yi Watsi Da Ayyuka Na Fiye Da Naira Tiriliyan 17 A Nijeriya – Cibiyar CIPMN

Bayanan ya nuna cewa jihohin sun kashe naira biliyan 9 zuwa naira biliyan 20 a kowacce wata, wanda ya ninka bashin da ake bi sakamakon faduwar darajar naira.
A watan Janairun 2024, jihohin Nijeriya sun kashe naira biliyan 9.88 wajen biyan basussuka a waje, wanda ya ragu daga naira biliyan 13.7 a watan Janairun 2023. A nan an sami ragowar kashi 27.7%, wanda yake nuna cewa wasu jihohi ba su da basussukan sosai.

 

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Haka kuma canjin dala na tsakanin naira 830 zuwa 1,000 wanda shi ne mafi kankanta a wannan rahoton.

A watan Fabrarun 2024 kuwa, an biya bashin naira biliyan 24.53, wanda aka sami karin kashi 148%, inda ya karu daga naira biliyan 9.88 na watan Fabrarun 2023.

 

A watan Maris 2024, an biya bashin naira biliyan 40.41, wanda hakan ke alamta cewa an sami karin kashe 309%, idan aka kwatanta da watan Maris ta 2023 da aka biya naira bilyan 9.88.

 

Daga watan Afrilu zuwa Yuni shekara ta 2024, jimillar bashin da aka biya shi ne, naira biliyan 21.70 a kowacce wata idan aka kwatanta da naira biliyan 9.88 da aka biya na shekarar 2023, kudin da aka kashe ya karu da kashi 119.70% a kowacce wata.

 

Jihohin Kaduna da Lagos su ne suka fio biyan bashi a kan kowacce jiha, don bashin da jihohin suka biya ya karu daga naira biliyan 16.88 a watannin shida na farkon shekarar 2023, inda a yanzu ya koma naira biliyan 32.44 a wannan shekarar ta 2024, Kenan an sami karin kashi 92%, wadannan jihohin guda biyu sun kashi 40% na bashin da ake binsu.

 

Haka kuma jihohin Kuros Ribas da Bauchi sun sami karin bashin da ake binsu. Inda Kuros Ribas ta biya Naira biliyan 2.21 a shekarar 2023 a wannan shekarar kuwa ya koma naira biliyan 7.87, an sami karin kashi 256%. A yayin da Jihar Bauchi a shekarar 2023 sun biya naira biliyan 3.28 a wannan shekarar kuwa sun biya naira biliyan 6.33 hakan na nuna cewa an sami karin kashi 93%.

 

Jihar Ogun sun sami karin biyan bashi a kasashen waje daga naira biliyan 1.57 a shekarar 2023 zuwa naira biliyan 4.29 a shekarar 2024, wanda aka sami karin kashi 173%, haka lamarin yake a Jihar Oyo inda abun ya karu daga naira biliyan 2.61 a shekarar 2023, ya koma naira biliyan 6.36 a shekarar 2024 wanda ke nuna an sami karin kashi 144%.

 

Jihar Ribas ma haka take don an sami karuwar bashi a kasashen waje daga naira biliyan 1.76 da aka biya a watannin shidar farkon shekara ta 2023 zuwa naira biliyan 4.62 a watanni shidar farkon shekara ta 2024, wanda ke nuna cewa an sami karin kashi 162% idan aka kwatanta shekarun.

 

Wadannan bayanan sun kara nuna yadda kudaden da Nijeriya ke samu suke karewa wajen biyan basussuka a waje.

Bashi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Bashi
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Next Post
Na Yi Mamakin Ganin Takardar Tuɓe Rawanina Na Sarautar Mujaddadin Bauchi – Sanata Buba

Na Yi Mamakin Ganin Takardar Tuɓe Rawanina Na Sarautar Mujaddadin Bauchi - Sanata Buba

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.