ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Yi Rashin Jagora, Buhari Ne Ya Ƙarfafa Min Guiwa Na Yi Takarar Gwamna A Kaduna — El-Rufai

by Muhammad
5 months ago
El-Rufai

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana marigayi tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari, a matsayin jagoran siyasarsa, wanda ya ƙarfafa masa guiwa har ya tsaya takarar gwamnan Kaduna.

A sakon ta’aziyyarsa, El-Rufai ya ce Buhari ya tsaya tsayin daka don ci gaban Nijeriya, ya bayar da gudummawa mai tsoka a matsayinsa na soja kuma shugaban ƙasa na mulkin soja da kuma zaɓaɓɓen shugaban ƙasa.

  • Rasuwar Buhari: Na Yi Rashin Ɗan’uwa, Aboki, Ɗan Ƙasa Nagari —Babangida
  • Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo

El-Rufai ya ce Buhari ya kasance jarumi mai juriya wanda duk da tsige shi daga mulki a 1985, ya dawo kuma ya lashe zaɓe a 2015.

ADVERTISEMENT

“Ko da yake bai cika magana ba, yana da natsuwa da barkwanci. Yana da hali mai sauƙi da ya sa talakawa ke ƙaunarsa, saboda suna ganin shi mutum ne mai gaskiya da amana.”

“Ko bayan faɗuwarsa a zaɓen shugaban ƙasa sau uku, ya sake tashi suka kafa jam’iyyar APC a 2013, wanda ya kayar da shugaban ƙasa mai ci a 2015. Ya kuma miƙa mulki cikin nasara a 2023, wanda hakan ya kafa tarihi.”

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Ya ƙara da cewa ya samu damar yin aiki da Buhari a jam’iyyar CPC bayan zaɓen 2011, inda Buhari ya sa shi ya jagoranci kwamitin farfado da jam’iyyar. Kwamitin ne ya ba da shawarar haɗakar CPC da ACN da sauran jam’iyyu don tunkarar zaɓen 2015.

“Shugaba Buhari shi ne jagoran siyasa ta. Shi ya karfafa min guiwa na tsaya takarar gwamnan Kaduna. Ya halarci ƙaddamar da kamfe ɗina a watan Nuwamba 2014, kuma ya tsaya min har na kai ga nasara. Ina godiya sosai da goyon bayansa a lokacin gwamnatina, har da damar da na samu na tattaunawa da shi a kowane lokaci, ko da kuwa muna da saɓani a wasu manufofi.”

El-Rufai ya roƙi Allah Ya gafarta wa Buhari, Ya sanya shi a Aljannatul Firdaus, tare da bai wa iyalansa, musamman Hajiya Aisha Buhari da ’ya’yansa, hakurin rashinsa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Shugaban ECOWAS Julius Bio, Ya Yi Wa Tinubu Da ‘Yan Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Buhari

Shugaban ECOWAS Julius Bio, Ya Yi Wa Tinubu Da 'Yan Nijeriya Ta'aziyyar Rasuwar Buhari

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.