• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NAFDAC Ta Yi Bikin Lalata Kayayyakin Jabu Na ₦985.3m A Kano

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Kiwon Lafiya, Labarai
0
Mutane 75,000 Sun Kamu Da HIV, 45,000 Sun Rasu A Shekarar 2023 – NACA DG
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta ƙasa (NAFDAC) ta lalata kayayyakin jabu, da marasa inganci, da wanda wa’adin aikinsa ya ƙare na kimanin Naira Miliyan ₦985.3m a jihar Kano.

Kayayyakin da aka lalata an karɓo su ne daga shiyyar Arewa maso Yamma, da suka haɗa da Kano da Katsina da Sokoto da Jigawa da Kaduna da kuma Zamfara, sun haɗa da magunguna marasa inganci, da kayan abinci marasa inganci, da kayan kwalliya, da sauran kayayyaki marasa inganci da hukumar NAFDAC ta haramta.

  • A Guji Ajiye Abinci A Firji Fiye Da Kwana 3 – NAFDAC
  • A Guji Ajiye Abinci A Firji Fiye Da Kwana 3 – NAFDAC

Darakta Janar ta Hukumar NAFDAC, Farfesa Mojisola Adeyeye, wacce ta samu wakilcin shugaban shiyyar Arewa maso Yamma, Uwargida Josephine Dayilim, ta bayyana cewa kayayyakin da aka lalata sun haɗa da maganin kashe kwayoyin cuta, da maganin hawan jini, da maganin zazzabin cizon sauro, da maganin kashe kasala, magungunan ganye, da abubuwan sha, da kayan kwalliya, da dai sauransu.

Wasu daga cikin kayan da aka lalata dai wasu ƙungiyoyi masu zaman kansu, da ƙungiyoyin Ƙwadago, da masu sayar da magunguna da kuma hukumar kwastam ta Najeriya ne suka miƙa su da kansa sakamakon ƙarewar wa’adin ingancinsu.

Hukumar ta jaddada ƙudirinta na kiyaye lafiyar jama’a da haɗa kai da masu ruwa da tsaki don tabbatar da sarrafa kayayyakin da aka kayyade.

Labarai Masu Nasaba

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

A cewarta, NAFDAC na da burin kiyaye aminci, da ingancin kayan abinci da magungunan da ake samarwa ga jama’a ta hanyar ƙarfafa ayyukanta.

Shugaban hukumar ta NAFDAC na jihar, Kasim Ibrahim, ya yi ƙarin haske kan tasirin masu sayar da miyagun kwayoyi ke da shi a kasuwannin saye da sayarwa zuwa cibiyar hada-hadar (CWC) da ke kasuwar Dangwauro.

Lalata wannan kaya ya yi nasarar daƙile yaɗuwar jabun kayayyaki da marasa inganci a jihar, wanda hakan ya amfanar da ɗaukacin yankin da ma sauran yankunan makwabta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: kanoNAFDAC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutane 75,000 Sun Kamu Da HIV, 45,000 Sun Rasu A Shekarar 2023 – NACA DG

Next Post

Summer Davos: An Tattauna “Sababbin Damammaki A Kasar Sin”

Related

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
Labarai

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

1 hour ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

3 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

4 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

5 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

10 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

12 hours ago
Next Post
davos

Summer Davos: An Tattauna "Sababbin Damammaki A Kasar Sin"

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.