• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NAHCON Ta Bai Wa Jihohi Wa’adin Awa 48 Da Su Tura Kudaden Aikin Hajjin 2023

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
NAHCON Ta Bai Wa Jihohi Wa’adin Awa 48 Da Su Tura Kudaden Aikin Hajjin 2023
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kula da aikin hajji ta kasa (NAHCON) ta bai wa hukumomi, rassa-rassa da suke da ruwa da tsaki a harkar biyan kudin hajji tare da hukumomin da ke kula da jin dadin Alhazai na jihohi wa’adin zuwa ranar Juma’a su tura dukkanin kudaden kujerar aikin Hajjin 2023.

Shugaban hukumar NAHCON, Alhaji Zikrullah Kunle Hassan, shi ne ya bayar da wannan wa’adin a jiya sa’ilin wata ganawa da manyan jami’an da ke kula da hukumomin kula da jin dadin Alhazai da sauran wadanda lamarin ya shafa da ya gudana a Hajj House, Abuja.

  • Hajjin 2023: Miliyan 3 Kowane Maniyyaci Zai Biya A Bana —NAHCON

A cewar sanarwar da mataimakiyar daraktan sashin yada labarai na hukumar NAHCON, Fatima Sanda Usara, ta ce, zaman ya cimma muhimman batutuwa da suka dabaibaye shigar da kudaden kujerar aikin Hajjin ta hanyar da daidaitawa da shigar da adadin maniyyatan da suka cancanta suka dace da za su samu tafiya daga Nijeriya.

A cewar sanarwar ta hanyar hakikance adadin ne za a rattaba hannun yarjejeniya da jiragen da za su yi jigilar.

Hassan ya ce, hukumar za ta yi amfani ne kawai da adadin kudin mutanen da aka shigar zuwa asusun da aka ware daga ranar Juma’a kuma da adadin ne za a sanya hannun yarjejeniya da kamfanonin jiragen saman da za su yi jigilar zuwa Saudiyya Arabiyya, kan hakan, duk kudin da bai shiga ba kafin ranar Juma’a ba zai samu tafiya aikin hajji na 2023.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

Shugaban ya yi bayanin cewa da zarar suka kammala cike sharudan yarjejeniya ana sa ran za su biya kamfanonin jiragen da za su yi jigilar alhazan kaso 50 cikin 100 yayin da kuma wani karin kaso 35 zai biyo bayan an turo jiragen domin fara aikin jigilar.

Ya nuna damuwarsa kan yadda har zuwa yanzu ba a shigar da kudaden ba sakamakon daukan lokaci.

Shugaban na NAHCON din ya kuma ce duk wani shirye-shiryen da za su yi ba zai kammala ba har sai bayan tabbatar da adadin wadanda suka biya kudinsu da niyyar tafiya.

Idan za a tuna dai an sha dage lokacin amsar kudaden Hajjin hajji a lokuta daban-daban tun a watan Janairun 2023 ake kara wa’adin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ma’aikatar Tsaron Jama’a Ta Kasar Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadi Game Da Matakin Hukumar Shari’ar Kasar Amurka

Next Post

PSC Ta Kori Jami’an ‘Yansanda 3 Kan Rashin Ladabi Da Biyayya

Related

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas
Manyan Labarai

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

33 minutes ago
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa
Labarai

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

3 hours ago
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Ra'ayi Riga

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

3 hours ago
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

6 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

15 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

16 hours ago
Next Post
Zargin Yaudara: Wani Tela Ya Kashe Tsohuwar Masoyiyarsa A Kaduna

PSC Ta Kori Jami'an 'Yansanda 3 Kan Rashin Ladabi Da Biyayya

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

August 26, 2025
ÆŠaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

ÆŠaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

August 26, 2025
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

August 26, 2025
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

August 26, 2025
ÆŠan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

ÆŠan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

August 26, 2025
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.