• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasarori Da Matsalolin Da NAHCON Ke Samu Wajen Gudanar Da Aikin Hajji

by Musa Muhammad Awwal
3 years ago
in Labarai
0
Nasarori Da Matsalolin Da NAHCON Ke Samu Wajen Gudanar Da Aikin Hajji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar yadda aka sani ne, NAHCON ce ke da alhakin shiryawa tare da gudanar da ayyukan da suka shafi aikin hajji a kasar nan, wanda kuma ita ce ke da alhakin ganin aikin ya gudana ba tare da wata tangarda ba.

Kamar kowace shekara, a bana ma Hukumar ta yi wannan aiki, inda kuma aka samu nasarori masu yawan gaske. Haka kuma, babu yadda za a yi a ce an yi wannan aiki ba tare wata matsala ba.

  • Shugaba Buhari Zai Kawo Karshen Rashin Tsaro A Nijeriya -Buratai
  • Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne

Game da korafin da wasu ke yi na cewa an bar wasu maniyyata a kasa ba su samu tafiya aikin hajjin ba, wannan ba abin korafi ba ne domin Hukumar ta sha bayyana cewa ba duk wanda ya biya kudinsa ne zai samu tafiya ba, don haka ne ma ake fada ma jama’a don su zama cikin shiri.

Saboda haka ga duk mai bibiyar aikin Hajji a duk shekara, sam wannan ba abu ne da ya kamata ya zama abin korafi ba, musamman bisa la’akari da yadda ita kanta Hukumar kasar Sadiyya ta ke rage yawan maniyyatan a duk shekara.

Wani abu mai daure kai kuma shi ne yadda ake samun korafi daga wasu ma’aikatan Hukumar wadanda ba su samu damar zuwa kasar mai tsarki don gudanar ayyukan da aka saba ba, alhali a bayyana ya ke, cewa ba duk ma’aikatan ne za a dade a tafi ba, dole akwai wadanda za a bari a ofis don wasu ayyukan.

Labarai Masu Nasaba

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

Bugu da kari, duk wani ma’aikacin da bai samu nasarar tafiya aikin hajjin ba, to akwai wani dan ihsani da ake yi masu a zaman da suke yi a kasar nan.

Amma sai ya zama duk da irin kyakkyawan tsarin da ake da shi wajen zabar ma’aikatan da za su tafi aikin hajjin, abin takaci, sai ya zama wasu suna fusata, har suna shiga kafafen yada labarai sun yin wadansu zarge-zarge marasa tushe.

Haka kuma, rikici ko rashin jituwar da kan faru tsakanin Hukumomin kula da jin dadin Alhazai na jihohi na daga cikin abubuwan da kan kawo tsaiko a harkar jigilar maniyyatan.

Wani babban misali, shi ne irin wanda aka samu tsakanin jihar Kano da kamfanin jirage na Azaman air, da kuma tsakanin jihar Kanon dai da adashen gata, alhali ita NAHCON ta riga ta yi kyakkyawan shiri a kan haka, wanda hakan ya kawo matsaloli.

Saboda haka ga duk wanda ya san irin namijin kokarin da NAHCON ke yi wajen ganin an samu aikin hajji mai cike da nasara, to ba zai damu da wasu kananan maganganu da wasu masu son zuciya ke yi ba.

Ina ganin bisa kyawawan tsare-tsaren da hukumar nan ke yi a duk shekara, to lallai ta cancanci jinjina ne ta musamman, musamman a ‘yan shekarun nan da suka gabata, wanda hakan ya sa suke samun lambar yabo bisa hukumar da ta yi fice wajen iya gabatar da tsari a aikin hajjin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aikin Hajjin BanaAlhazaiCi GabaJirageMahajjataNAHCONSaudiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kungiyar Kawance Ta Sin Da Niger Na Goyon Bayan Manufar Sin Daya Tak

Next Post

“Korar Fulani A Edo: Ina Ake So Wadanda Aka Haifa A Jihar Shekara 50 Su Koma?”

Related

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

1 hour ago
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

3 hours ago
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa
Labarai

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

4 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

5 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

6 hours ago
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 
Labarai

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

15 hours ago
Next Post
“Korar Fulani A Edo: Ina Ake So Wadanda Aka Haifa A Jihar Shekara 50 Su Koma?”

“Korar Fulani A Edo: Ina Ake So Wadanda Aka Haifa A Jihar Shekara 50 Su Koma?”

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.