ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasarori Da Matsalolin Da NAHCON Ke Samu Wajen Gudanar Da Aikin Hajji

by Musa Muhammad Awwal
4 years ago
NAHCON

Kamar yadda aka sani ne, NAHCON ce ke da alhakin shiryawa tare da gudanar da ayyukan da suka shafi aikin hajji a kasar nan, wanda kuma ita ce ke da alhakin ganin aikin ya gudana ba tare da wata tangarda ba.

Kamar kowace shekara, a bana ma Hukumar ta yi wannan aiki, inda kuma aka samu nasarori masu yawan gaske. Haka kuma, babu yadda za a yi a ce an yi wannan aiki ba tare wata matsala ba.

  • Shugaba Buhari Zai Kawo Karshen Rashin Tsaro A Nijeriya -Buratai
  • Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne

Game da korafin da wasu ke yi na cewa an bar wasu maniyyata a kasa ba su samu tafiya aikin hajjin ba, wannan ba abin korafi ba ne domin Hukumar ta sha bayyana cewa ba duk wanda ya biya kudinsa ne zai samu tafiya ba, don haka ne ma ake fada ma jama’a don su zama cikin shiri.

ADVERTISEMENT

Saboda haka ga duk mai bibiyar aikin Hajji a duk shekara, sam wannan ba abu ne da ya kamata ya zama abin korafi ba, musamman bisa la’akari da yadda ita kanta Hukumar kasar Sadiyya ta ke rage yawan maniyyatan a duk shekara.

Wani abu mai daure kai kuma shi ne yadda ake samun korafi daga wasu ma’aikatan Hukumar wadanda ba su samu damar zuwa kasar mai tsarki don gudanar ayyukan da aka saba ba, alhali a bayyana ya ke, cewa ba duk ma’aikatan ne za a dade a tafi ba, dole akwai wadanda za a bari a ofis don wasu ayyukan.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Bugu da kari, duk wani ma’aikacin da bai samu nasarar tafiya aikin hajjin ba, to akwai wani dan ihsani da ake yi masu a zaman da suke yi a kasar nan.

Amma sai ya zama duk da irin kyakkyawan tsarin da ake da shi wajen zabar ma’aikatan da za su tafi aikin hajjin, abin takaci, sai ya zama wasu suna fusata, har suna shiga kafafen yada labarai sun yin wadansu zarge-zarge marasa tushe.

Haka kuma, rikici ko rashin jituwar da kan faru tsakanin Hukumomin kula da jin dadin Alhazai na jihohi na daga cikin abubuwan da kan kawo tsaiko a harkar jigilar maniyyatan.

Wani babban misali, shi ne irin wanda aka samu tsakanin jihar Kano da kamfanin jirage na Azaman air, da kuma tsakanin jihar Kanon dai da adashen gata, alhali ita NAHCON ta riga ta yi kyakkyawan shiri a kan haka, wanda hakan ya kawo matsaloli.

Saboda haka ga duk wanda ya san irin namijin kokarin da NAHCON ke yi wajen ganin an samu aikin hajji mai cike da nasara, to ba zai damu da wasu kananan maganganu da wasu masu son zuciya ke yi ba.

Ina ganin bisa kyawawan tsare-tsaren da hukumar nan ke yi a duk shekara, to lallai ta cancanci jinjina ne ta musamman, musamman a ‘yan shekarun nan da suka gabata, wanda hakan ya sa suke samun lambar yabo bisa hukumar da ta yi fice wajen iya gabatar da tsari a aikin hajjin.

NAHCON
Musa Muhammad Awwal
+ postsBio

    MASU ALAKA

    Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
    Manyan Labarai

    Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

    June 24, 2026
    ‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
    Manyan Labarai

    ’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

    June 24, 2026
    Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
    Labarai

    Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

    June 24, 2026
    Next Post
    “Korar Fulani A Edo: Ina Ake So Wadanda Aka Haifa A Jihar Shekara 50 Su Koma?”

    “Korar Fulani A Edo: Ina Ake So Wadanda Aka Haifa A Jihar Shekara 50 Su Koma?”

    LABARAI MASU NASABA

    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

    June 24, 2026
    Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

    Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

    June 24, 2026
    Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

    Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

    June 24, 2026
    Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

    Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

    June 24, 2026
    ‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

    ’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

    June 24, 2026
    Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

    Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

    June 24, 2026
    An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

    An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

    June 24, 2026
    Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

    Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

    June 24, 2026
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

    June 23, 2026
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

    June 23, 2026

    © 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

    No Result
    View All Result
    • Gida
    • Labarai
      • Manyan Labarai
      • Kananan Labarai
      • Masarautu
      • Bakon Marubuci
      • Dausayin Musulunci
      • Daga Kasar Sin
      • Nishadi
      • Noma Da Kiwo
      • Sana’a Sa’a
      • Tambarin Dimokuradiyya
      • Taskira
      • Daga Birnin Sin
      • Ado Da Kwalliya
    • Siyasa
    • Wasanni
    • Al’adu
    • Al’ajabi
    • Labaran Kasuwanci
    • Karanta cikin Turanci

    © 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.