ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasarori Da Matsalolin Da NAHCON Ke Samu Wajen Gudanar Da Aikin Hajji

by Musa Muhammad Awwal
4 years ago
NAHCON

Kamar yadda aka sani ne, NAHCON ce ke da alhakin shiryawa tare da gudanar da ayyukan da suka shafi aikin hajji a kasar nan, wanda kuma ita ce ke da alhakin ganin aikin ya gudana ba tare da wata tangarda ba.

Kamar kowace shekara, a bana ma Hukumar ta yi wannan aiki, inda kuma aka samu nasarori masu yawan gaske. Haka kuma, babu yadda za a yi a ce an yi wannan aiki ba tare wata matsala ba.

  • Shugaba Buhari Zai Kawo Karshen Rashin Tsaro A Nijeriya -Buratai
  • Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne

Game da korafin da wasu ke yi na cewa an bar wasu maniyyata a kasa ba su samu tafiya aikin hajjin ba, wannan ba abin korafi ba ne domin Hukumar ta sha bayyana cewa ba duk wanda ya biya kudinsa ne zai samu tafiya ba, don haka ne ma ake fada ma jama’a don su zama cikin shiri.

ADVERTISEMENT

Saboda haka ga duk mai bibiyar aikin Hajji a duk shekara, sam wannan ba abu ne da ya kamata ya zama abin korafi ba, musamman bisa la’akari da yadda ita kanta Hukumar kasar Sadiyya ta ke rage yawan maniyyatan a duk shekara.

Wani abu mai daure kai kuma shi ne yadda ake samun korafi daga wasu ma’aikatan Hukumar wadanda ba su samu damar zuwa kasar mai tsarki don gudanar ayyukan da aka saba ba, alhali a bayyana ya ke, cewa ba duk ma’aikatan ne za a dade a tafi ba, dole akwai wadanda za a bari a ofis don wasu ayyukan.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Bugu da kari, duk wani ma’aikacin da bai samu nasarar tafiya aikin hajjin ba, to akwai wani dan ihsani da ake yi masu a zaman da suke yi a kasar nan.

Amma sai ya zama duk da irin kyakkyawan tsarin da ake da shi wajen zabar ma’aikatan da za su tafi aikin hajjin, abin takaci, sai ya zama wasu suna fusata, har suna shiga kafafen yada labarai sun yin wadansu zarge-zarge marasa tushe.

Haka kuma, rikici ko rashin jituwar da kan faru tsakanin Hukumomin kula da jin dadin Alhazai na jihohi na daga cikin abubuwan da kan kawo tsaiko a harkar jigilar maniyyatan.

Wani babban misali, shi ne irin wanda aka samu tsakanin jihar Kano da kamfanin jirage na Azaman air, da kuma tsakanin jihar Kanon dai da adashen gata, alhali ita NAHCON ta riga ta yi kyakkyawan shiri a kan haka, wanda hakan ya kawo matsaloli.

Saboda haka ga duk wanda ya san irin namijin kokarin da NAHCON ke yi wajen ganin an samu aikin hajji mai cike da nasara, to ba zai damu da wasu kananan maganganu da wasu masu son zuciya ke yi ba.

Ina ganin bisa kyawawan tsare-tsaren da hukumar nan ke yi a duk shekara, to lallai ta cancanci jinjina ne ta musamman, musamman a ‘yan shekarun nan da suka gabata, wanda hakan ya sa suke samun lambar yabo bisa hukumar da ta yi fice wajen iya gabatar da tsari a aikin hajjin.

NAHCON
Musa Muhammad Awwal
+ postsBio

    MASU ALAKA

    An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
    Labarai

    An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

    September 9, 2026
    Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
    Manyan Labarai

    Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

    September 9, 2026
    ’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
    Manyan Labarai

    ’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

    September 9, 2026
    Next Post
    “Korar Fulani A Edo: Ina Ake So Wadanda Aka Haifa A Jihar Shekara 50 Su Koma?”

    “Korar Fulani A Edo: Ina Ake So Wadanda Aka Haifa A Jihar Shekara 50 Su Koma?”

    LABARAI MASU NASABA

    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

    September 9, 2026
    An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

    An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

    September 9, 2026
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

    September 9, 2026
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

    September 9, 2026
    Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

    Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

    September 9, 2026
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

    September 9, 2026
    Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

    Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

    September 9, 2026
    “Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

    “Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

    September 9, 2026
    ’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

    ’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

    September 9, 2026
    Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

    Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

    September 9, 2026

    © 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

    No Result
    View All Result
    • Gida
    • Labarai
      • Manyan Labarai
      • Kananan Labarai
      • Masarautu
      • Bakon Marubuci
      • Dausayin Musulunci
      • Daga Kasar Sin
      • Nishadi
      • Noma Da Kiwo
      • Sana’a Sa’a
      • Tambarin Dimokuradiyya
      • Taskira
      • Daga Birnin Sin
      • Ado Da Kwalliya
    • Siyasa
    • Wasanni
    • Al’adu
    • Al’ajabi
    • Labaran Kasuwanci
    • Karanta cikin Turanci

    © 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.