• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

by Abubakar Abba
5 months ago
Gona

Ana samun amfanin gona da dama a Nijeriya da ke girma cikin ‘yan watanni kadan. Mun yi muku nazari a kan amfanin gona takwas da ake girbewa cikin wata shida ko kasa da haka kamar haka:

Waken Suya: Waken Suya na daya daga cikin amfanin gona masu gina jikin dan Adam, yana kuma dauke da sanadarin ‘protein’. Kamar yadda aka sani, ana dafa Waken Suya sannan ana sarrafa busashensa a yi Madara, Fulawa, Awara da sauran nau’ikan abinci.

  • Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta
  • Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

Haka nan, ana kuma sarrafa shi zuwa Mai, sannan ana kuma ciyar da dabbobi da da shi. Bayan an shuka Irin sa, ana girbe shi daga wata uku zuwa biyar, amma ya danganta da irin yanayi da kuma nau’in Irin nasa da aka shuka.

Shinkafa: Irin Shinkafa da ake shukawa na kaiwa daga watanni Uku zuwa biyar kafin ta girma. Kazalika, tana da saurin yin girma tana kuma kaiwa tsawon kafa uku bayan kwanaki 120, wanda ya yi daidai da lokacin girbe ta, tana kuma samun karbuwa a kasuwannin Nijeriya yadda ya kamata.

Masara: Masara na daya daga cikin amfanin gona da ake yin amfani da ita a matsayin abinci a Nijeriya, sannan ana kuma gasa ta domin ci tare da sarrafa ta zuwa Gurguru. Har wa yau, ana kuma sarrafa ta zuwa fulawa da sauran makamantansu tare da sarrafa ta zuwa abincin dabbobi.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

Akasari kafin a girbe ta, tana kaiwa kwanaki 60 zuwa 100 bayan an shuka ta. Kazalika, cikin sauki ake mallakar gonar da ake shuka Masara a Nijeriya, ana kuma shuka Irinta sannan a sayar da ita ga makwabta.

Dankali: Dankali na dauke da sinadarin ‘calories’ dan kadan, sannan mutane da dama na kasar nan na sarrafa shi a matayin abinci tare da yin amfani da shi. Yana daukar watanni biyu zuwa uku bayan an shuka shi. Bugu da kari, ana iya shuka shi a kowacce irin kasar noma.

Tumatir: Ana matukar amfani da tumatir a Nijeriya, ko danyensa ko kuma busasshe. Yana dauke da sanadarin ‘bitamin C’, yana kuma taimakawa wajen rage kamuwa da cututtuka kamar wadanda ke yi wa zuciya illa, ciwon siga da kuma cutar daji.

Ana son a shuka Irinsa a kasar noma mai kyau tare da yi masa ban ruwa. Bayan an shuka Irin nasa, ana fara girbe shi daga watanni 2 zuwa 3, ya danganta da nau’in Irin da aka yi amfani da shi wajen shukawa.

Kankana: Duk yayin da aka shuka Irin Kankana, cikin dan gajeren lokaci ake girbe ta. A Nijeriya, daga wata 3 ake fara girbe ta, sannan ana iya shuka Irinta a kowanne bangare na fadin wannan kasa. Wakazalika, kankana na dauke da sinadarin ‘bitamin A’ da kuma ‘bitamin C’ mai yawan gaske.

Tattasai: Bayan shuka Irin tattasai, ana girbe shi cikin watanni uku kacal. Kazalika, ana iya cewa kusan kowane gida a fadin Nijeriya na yin amfani da shi. Ana kuma sayar da tattasai a kasuwanni da dama a wannan kasa, sannan wadanda ke yin sana’arsa na matukar samun rufin asiri ko kudaden shiga. Hatta a bayan dakin gidanka, za ka iya shuka Irin Tattasai ya girma ya kuma bayar da abin da ake so.

8. Kokumba: Kokumba na daya daga cikin sanannin kayan marmari ko lambu, ana kuma yin noman sa a wurare da dama na fadin Nijeriya. Wasu na cin sa tsurarsa, domin alfanun da yake da shi musamman a fannin kiwon lafiya. A duk lokacin da aka shuka Irinsa yana da matukar saurin yin girma, ana kuma girbe shi bayan akalla watanni 3. Sannan yana da saurin tafiya a kasuwa, ma’ana mutane suna son sa kwarai da gaske sakamakon amfaninsa ga lafiyar dan Adam.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI
Noma Da Kiwo

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
Next Post
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Ba Za A Samu Ƙarancin Man Fetur A Lokutan Bukukuwan Ƙarshen Shekara Ba – Dangote 

October 27, 2025
An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

October 27, 2025
Gona

Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.