ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan

by Abubakar Abba
2 years ago
Brazil

Gwamnatin tarayya tare da kamfanin sarrafa takin zamani ‘Fundação Getulio Bargas’ na Kasar Brazil, sun rattaba hannu kan yarjejeniyar sarrafa takin zamani da samar da ingantacen Iri da kuma kudade ga fannin aikin noma a Nijeriya.

Sun sanya hanun ta hanyar ma’aikatar samar da wadataccen abinci na wannan kasa.

  • Halartar Shugaba Xi Taron APEC Da G20, Da Ziyarar Aiki A Peru Da Brazil Sun Kasance Wata Hanyar Sada Zumunta Da Hadin Gwiwa
  • An Yi Wa Shugaban Ƙasar Brazil Lula Da Silva Tiyatar Ƙwaƙwalwa 

Hakan na kunshen ne cikin sanarwar da fadar shugaban kasa ta fitar, wacce Daraktan Yada Labarai da Hurda da Jama’a; Abiodun Oladunjoye ya fitar a Abuja.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta bayyana cewa, Babban Sakataren Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wataceccen Abinci, Farfesa Carlos Iban Simonsen ne ya rabbata hannun a madadin gwamnatin tarayya.

An rattaba hannun ne, a Birnin Rio de Janeiro na kasar ta Brazil a bayan fagen taron shugabanin kasashen duniya 20 masu karfin tattalin arziki a duniya.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Kazalika, sanarwar ta sanar da cewa; rattaba hannun ya bode wani sabon fage a tsakanin Nijeriya da aikin da ake yi na amfani da fasahar zamani, don kara bunkasa fannin aikin noma a fadin wannan kasa.

A cewar sanarwar, aikin wanda aka faro tun a shekarar 2018, zai lashe kimanin dala biliyan 1.2, wanda kuma da ma hadaka ce tsakanin Nijeriya da kasar ta Brazil.

Haka zalika, an tsara aikin ne don kara habaka fannin aikin noma na kasar nan, ta hanyar yin amfani da kwararrun da suka fito daga Kasar Brazil.

Har wa yau, sanarwar ta sanar da cewa; bankin Deutsche na inganata aikin noma ta hanyar amfani da fasahar zamani da kuma yada ilimin aikin noman nan da zuwa shekaru goma masu zuwa.

Nan da shekaru biyar masu zuwa, aikin zai gano tare kuma da tallafawa aikin noma a kananan hukumomi 774 tare da bai wa manoman tallafin kudi, domin kara habaka fannin aikin noma da tattalin arziki.

Fashedemi ya sanar da cewa, wannan hadaka; za ta bai wa Kasar Brazil damar jawo Nijeriya a jiki, musamman don gaggauta bunkasa fannin aikin noma a kasar.

A cewar tasa, ta hanyar haka ne za mu samu damar fito da albarkar da ke fannin zuba hannun jari a manyan ayyuka, musamman don samar da wadataccen abinci.

A karkashin yarjejeniyar, masu zaman kansu a fannin sarrafa takin zamani da samar da ingantaccen Iri, ana sa ran za su samu kudaden shiga kimanin dala biliyan 4.3.

Brazil
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Nazari Kan Cututtuka 8 Da Ke Kama Zomo Da Hanyoyin Mangance Su

Nazari Kan Cututtuka 8 Da Ke Kama Zomo Da Hanyoyin Mangance Su

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.