• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NCRMIDP Ta Raba Wa ‘Yan Gudun Hijira 700 Kayan Abinci A Katsina

by Muhammad
1 year ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
NCRMIDP Ta Raba Wa ‘Yan Gudun Hijira 700 Kayan Abinci A Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kula da ‘yan gudun hijira da bakin haure da ‘yan gudun hijira ta kasa NCRMIDP ta raba wasu kayan abinci ga mata sama da 700 da suka rasa matsugunansu a jihar Katsina.

Kwamishinan tarayya na NCRMIDP, Hon. Tijjani Aliyu Ahmed, ne ya jagoranci tawagar zuwa Katsina domin rabon kudade ga wadanda suka amfana a karshen mako, ya fara ziyarar Gwamna Umaru Dikko Radda a ofishinsa.

  • Rundunar Sojin Sama Ta Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama Tare Da Lalata Maboyarsu A Katsina Da Zamfara
  • Gwamnati Katsina Ta Kashe Miliyan 50 Wajen Gyara Motocin ‘Yansanda 15

Ahmed ya sanar da gwamnan irin ayyukan da Hukumar ke gudanarwa, musamman shirinta na samar da cibiyoyin horar da ‘yan kasuwa a fadin shiyyoyin kasar nan.

Da yake nuna damuwarsa kan yawaitar ayyukan ‘yan bindiga a jihar da ke kara yawan ‘yan gudun hijira a kullum, Ahmed ya bayyana cewa gwamnati na da shirin bai wa ‘yan gudun hijirar damar dogaro da kansu.

Ya ce tuni Hukumar ta horas da yara kimanin 120 da suka rasa matsugunnansu, yayin da kuma aka bai wa mata 70 jari don samun ingantacciyar rayuwa da gina rijiyoyin burtsasai masu amfani da wutar lantarki mai amfani da hasken rana a sansanonin su.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

Kwamishinan na tarayya ya nemi hadin kan gwamnatin jihar domin a yi amfani da cibiyoyin tsugunar da ‘yan gudun hijira da aka gina kwanan nan, inda ya ce ayyukan ‘yan fashin na ba mutane tsoro.

Ya godewa gwamnatin jihar bisa kokarinta na bayar da tallafi ga ‘yan gudun hijira tare da yaki da matsalar ‘yan fashi a jihar.

Shi ma da yake nasa jawabin, Gwamna Radda, ya godewa hukumar kan goyon bayan da take bayar wa, yana mai jaddada cewa gwamnatinsa ta riga ta dukufa wajen ganin an shawo kan matsalolin jama’a.

Radda ya kuma shaida cewa, gwamnati ta kulla kawance da hukumar raya kasashe ta Majalisar Dinkin Duniya UNDP, ciki har da hukumar kula da ‘yan gudun hijira a wani yunkuri na rage matsalolin da ‘yan gudun hijira ke fuskanta da samar da mafita mai dorewa don sake dawo da su tare da karfafa musu guiwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KatsinaKayan AbinciNCRMIDP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ramadan: Gwamnatin Jigawa Za Ta Ciyar Da Mutum 171,900 A Kullum Da Azumi – Namadi

Next Post

Mulkin Kama-karya Ne Ke Sa Wawason Kayan Abinci – Jam’iyyar PRP

Related

Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

22 hours ago
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi
Da ɗumi-ɗuminsa

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

2 days ago
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

2 days ago
Farfesa Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa
Da ɗumi-ɗuminsa

Farfesa Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

3 days ago
Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba

5 days ago
Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano

5 days ago
Next Post
PRP

Mulkin Kama-karya Ne Ke Sa Wawason Kayan Abinci – Jam’iyyar PRP

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Katsina

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.