ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Ɗumi-Ɗumi: Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Shugabannin Ƙungiyar Ansaru 2

by Sadiq
11 months ago
Ansaru

Mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, ya sanar da cewa jami’an tsaro sun kama manyan shugabannin ƙungiyar ‘yan ta’adda ta Ansaru bayan watanni ana nemansu ruwa a jallo.

Waɗanda aka kama sun haɗa da Mahmud Muhammad Usman, wanda aka fi sani da Abu Baraa, wanda shi ne shugaban ƙungiyar, da kuma mataimakinsa Mahmud al-Nigeri, wanda aka fi sani da Mallam Mamuda.

  • Hadin Tuwon Dawa
  • APC Ta Nemi A Soke Zaɓen Cike Gurbi A Kano Saboda Rikici

Ribadu ya ce dukkanninsu sun shafe shekaru suna cikin jerin waɗanda ake nema bisa laifin kai wa  jami’an tsaro da mutane hare-hare da gine-ginen gwamnati.

ADVERTISEMENT

A lokacin da yake jawabi a Abuja ranar Asabar, Ribadu ya bayyana wannan a matsayin babban ci gaba a yaƙi da ta’addanci a Nijeriya.

Ya ce Abu Baraa shi ne yake kiran kansa “Sarkin Ansaru” tare da sama maɓoyar ta’addanci a sassa daban-daban na ƙasar nan.

LABARAI MASU NASABA

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

Ya kuma jagoranci sace mutane da fashi don tara kuɗaɗen da suke amfani da su wajen aikata ta’addanci.

Mataimakinsa Mamuda shi ne ke jagorantar rukunin “Mahmudawa” wanda ke aiki a kusa da Kainji National Park da ke tsakanin Jihar Neja da Kwara har zuwa Jamhuriyar Benin.

Ribadu ya ce Mamuda ya samu horo a Libya tsakanin shekarun 2013 da 2015, inda ya koyi amfani da makamai da kuma haɗa bama-bamai.

Ƙungiyar Ansaru ta fara ne a shekarar 2012 bayan ta ɓalle daga Boko Haram.

A farko ta yi ikirarin jihadi, amma daga baya ta fara kai wa jami’an tsaro, al’umma, da kuma gine-ginen gwamnati hare-hare.

Ƙungiyar kuma tana da alaƙa da Al-Qaeda a Arewacin Afirka.

A tsawon shekaru, ana danganta ƙungiyar da manyan laifuka da suka haɗa da balle gidan yarin Kuje a 2022, harin wajen haƙar uranium a Nijar, sace injiniyan Faransa Francis Collomp a 2013, sace Alhaji Musa Umar Uba na Daura a 2019, da kuma sace Sarkin Wawa.

Ribadu ya ce har yanzu suna da alaƙa da ƙungiyoyin ta’addanci a Mali, Nijar da Burkina Faso.

Ministan Watsa Labaru, Mohammed Idris, ya buƙaci ‘yan Nijeriya da su riƙa bai wa jami’an tsaro bayanai masu amfani don kawo ƙarshen ta’addanci.

Ya kuma roƙi kafafen yaɗa labarai kada su riƙa yaɗa manufar ‘yan ta’addan domin samun karɓuwa.

MASU ALAKA

inec
Manyan Labarai

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta
Manyan Labarai

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Manyan Labarai

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026
Next Post
Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta

Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta

LABARAI MASU NASABA

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026
inec

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina

July 12, 2026
Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.