ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Ɗumi-Ɗumi: Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Shugabannin Ƙungiyar Ansaru 2

by Sadiq
10 months ago
Ansaru

Mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, ya sanar da cewa jami’an tsaro sun kama manyan shugabannin ƙungiyar ‘yan ta’adda ta Ansaru bayan watanni ana nemansu ruwa a jallo.

Waɗanda aka kama sun haɗa da Mahmud Muhammad Usman, wanda aka fi sani da Abu Baraa, wanda shi ne shugaban ƙungiyar, da kuma mataimakinsa Mahmud al-Nigeri, wanda aka fi sani da Mallam Mamuda.

  • Hadin Tuwon Dawa
  • APC Ta Nemi A Soke Zaɓen Cike Gurbi A Kano Saboda Rikici

Ribadu ya ce dukkanninsu sun shafe shekaru suna cikin jerin waɗanda ake nema bisa laifin kai wa  jami’an tsaro da mutane hare-hare da gine-ginen gwamnati.

ADVERTISEMENT

A lokacin da yake jawabi a Abuja ranar Asabar, Ribadu ya bayyana wannan a matsayin babban ci gaba a yaƙi da ta’addanci a Nijeriya.

Ya ce Abu Baraa shi ne yake kiran kansa “Sarkin Ansaru” tare da sama maɓoyar ta’addanci a sassa daban-daban na ƙasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Ya kuma jagoranci sace mutane da fashi don tara kuɗaɗen da suke amfani da su wajen aikata ta’addanci.

Mataimakinsa Mamuda shi ne ke jagorantar rukunin “Mahmudawa” wanda ke aiki a kusa da Kainji National Park da ke tsakanin Jihar Neja da Kwara har zuwa Jamhuriyar Benin.

Ribadu ya ce Mamuda ya samu horo a Libya tsakanin shekarun 2013 da 2015, inda ya koyi amfani da makamai da kuma haɗa bama-bamai.

Ƙungiyar Ansaru ta fara ne a shekarar 2012 bayan ta ɓalle daga Boko Haram.

A farko ta yi ikirarin jihadi, amma daga baya ta fara kai wa jami’an tsaro, al’umma, da kuma gine-ginen gwamnati hare-hare.

Ƙungiyar kuma tana da alaƙa da Al-Qaeda a Arewacin Afirka.

A tsawon shekaru, ana danganta ƙungiyar da manyan laifuka da suka haɗa da balle gidan yarin Kuje a 2022, harin wajen haƙar uranium a Nijar, sace injiniyan Faransa Francis Collomp a 2013, sace Alhaji Musa Umar Uba na Daura a 2019, da kuma sace Sarkin Wawa.

Ribadu ya ce har yanzu suna da alaƙa da ƙungiyoyin ta’addanci a Mali, Nijar da Burkina Faso.

Ministan Watsa Labaru, Mohammed Idris, ya buƙaci ‘yan Nijeriya da su riƙa bai wa jami’an tsaro bayanai masu amfani don kawo ƙarshen ta’addanci.

Ya kuma roƙi kafafen yaɗa labarai kada su riƙa yaɗa manufar ‘yan ta’addan domin samun karɓuwa.

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa
Manyan Labarai

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Tsaurara Tsaro A NIPSS Bayan Harin ’Yan Bindiga

June 19, 2026
Next Post
Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta

Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Wasa 23 Da Eric Chelle Ya Gayyata Domin Buga Wasannin Sada Zumunci 

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

June 20, 2026
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.