• English
  • Business News
Monday, May 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Gudanar Da Bikin Ranar Yaki Da Sha Da Fataucin Miyagun Kwayoyi Na Duniya A Kebbi

by Sadiq
3 years ago
in Labarai
0
NDLEA Ta Gudanar Da Bikin Ranar Yaki Da Sha Da Fataucin Miyagun Kwayoyi Na Duniya A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Hana Sha da Fataucin miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA), reshen Jihar Kebbi, ta bi sahun sauran jihohi da masu ruwa da tsaki wajen gudanar da bikin ranar yaki da fataucin miyagun kwayoyi ta duniya a jihar.

Bayan kudurin Majalisar Dinkin Duniya (MDD) a shekarar 1987, ranar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi na duniya da nufin karfafa aiki da hadin gwiwa don cimma burin al’ummar duniya da ba ta su ga muggan kwayoyi.

  • Mutane 3 Sun Mutu A Hatsarin Mota, Biyu Sun Jikkata A Kogi
  • G7 Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Taimakon Ukraine A Yakinta Da Rasha

Bikin na 2022 mai taken cewa” Magance kalubalen shan kwayoyi a cikin Lafiya da Rikicin Jin kai yana da matukar dacewa dangane da cutar ta Korona da karuwar kalubalen tsaro a Nijeriya”.

 

A shekarar 2021, NDLEA ta kama sama da tan bakwai na haramtattun kwayoyi da kudinsu ya haura Naira Biliyan 130 tare da gurfanar da mutane sama da 900 da ake zargi.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto

Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe

A nasa jawabin, Kwamandan NDLEA na shiyyar Sokoto, Kebbi da Zamfara, Muhammad Misbahu Idris, ya yabawa kokarin mai girma Sanata Abubakar Atiku Bagudu, da uwar gidansa Dakta Zainab Shinkafi Bagudu,  bisa gagarumin goyon baya da gudunmawar da suke bayarwa a Jihar Kebbi wajen ganin an magance matsalar na shan miyagun kwayoyi a fadin Jihar.

Haka kuma ya ce” yawaitar shaye-shayen miyagun kwayoyi a Nijeriya ya yi yawa, kafin yawan shan muggan kwayoyi a duniya ya kai kashi 15 cikin 100 amma a Nijeriya a yau ya kai kashi 15.

Haka zalika, ya yi kira ga iyaye da masu ruwa da tsaki da su zage damtse wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansu wajen kula da ‘ya’yansu da kyau don kaucewa ga fadawa cikin shan miyagun kwayoyi ko kuma abokantaka da Matasa masu shaye shaye.

Bugu da kari, ya yi kira ga jami’an hukumarsa da su kara kaimi wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansu na kamawa da gurfanar da masu aikata laifin shan miyagun kwayoyi.

Tun da farko, kwamishinan ma’aikatar kiwon lafiya na jihar, Jafar Muhammad, wanda ya wakilci gwamnan jihar Kebbi, ya yi alkawarin ci gaba da bayar da goyon bayan gwamnatin jihar domin dakile ta’ammali da miyagun kwayoyi a jihar.

A wani bangare na bikin rana, an gudanar da atisayen tafiya da kafa da rera wakoki daga ofishin jiha zuwa fadar Sarkin Gwandu, daga nan sai suka zarce zuwa masaukin fadar shugaban kasa, inda aka gudanar da lakcoci kan shaye-shayen miyagun kwayoyi da laifuka, da kuma haramcin shan miyagun kwayoyi a cikin al’umma.

Mahalarta taron, sun hada da sakatare na dindindin na Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kebbi, Wakilan Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa, Hukumar Kula da Lafiyar Jama’a ta Tarayya, Jami’an Hukumar Kare Hadura ta Kasa, Jami’an Tsaro da Tsaron Farar Hula, Kungiyoyin Sa-kai da Kungiyoyin Jama’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hukumar LafiyaKebbiKwamandaNDLEAShan Miyagun KwayoyiSokotoZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kafa Cibiyar Raya Al’Adu Da Tattalin Arzikin Sin Da Afrika A Fuzhou

Next Post

Dole Ne A Ci Gaba Da Binciken Alkalin Alkalai Mai Murabus, Tanko Muhammad — Majalisa

Related

Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto

2 minutes ago
Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe
Labarai

Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe

11 hours ago
An Cafke Mai Garkuwa Da Mutane A Sansanin Alhazan Abuja
Labarai

An Cafke Mai Garkuwa Da Mutane A Sansanin Alhazan Abuja

12 hours ago
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunana
Labarai

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunana

16 hours ago
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (I)
Labarai

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (I)

18 hours ago
Kano
Labarai

Zargin Kin Amincewar Kwankwaso Zuwa APC: Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Mai Taimaka Ma Ta

18 hours ago
Next Post
Dole Ne A Ci Gaba Da Binciken Alkalin Alkalai Mai Murabus, Tanko Muhammad — Majalisa

Dole Ne A Ci Gaba Da Binciken Alkalin Alkalai Mai Murabus, Tanko Muhammad — Majalisa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto

Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto

May 19, 2025
Tarihin Makarantar Katsina-kwalej Zuwa Ta Horon Malamai (1)

Tarihin Makarantar Katsina-kwalej Zuwa Ta Horon Malamai (1)

May 18, 2025
Abin Da Ya Dace Ki Yi Yayin Haila Da Bayan Kin Gama?

Abin Da Ya Dace Ki Yi Yayin Haila Da Bayan Kin Gama?

May 18, 2025
Ciwon Mara Lokacin Al’ada

Ciwon Mara Lokacin Al’ada

May 18, 2025
Kasar Sin Ta Samu Bunkasar Masana’antar Harkokin Tauraron Dan Adam A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Bunkasar Masana’antar Harkokin Tauraron Dan Adam A Shekarar 2024

May 18, 2025
Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe

Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe

May 18, 2025
An Cafke Mai Garkuwa Da Mutane A Sansanin Alhazan Abuja

An Cafke Mai Garkuwa Da Mutane A Sansanin Alhazan Abuja

May 18, 2025
Kasar Sin Ta Sanya Harajin Takaita Shigo Da Kayayyakin Robobi Masu Tauri

Kasar Sin Ta Sanya Harajin Takaita Shigo Da Kayayyakin Robobi Masu Tauri

May 18, 2025
Yadda Ake Hada Danderun Kaza

Yadda Ake Hada Danderun Kaza

May 18, 2025
Ban ÆŠauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

Ban ÆŠauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

May 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.