• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Gudanar Da Bikin Ranar Yaki Da Sha Da Fataucin Miyagun Kwayoyi Na Duniya A Kebbi

by Sadiq
3 years ago
in Labarai
0
NDLEA Ta Gudanar Da Bikin Ranar Yaki Da Sha Da Fataucin Miyagun Kwayoyi Na Duniya A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Hana Sha da Fataucin miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA), reshen Jihar Kebbi, ta bi sahun sauran jihohi da masu ruwa da tsaki wajen gudanar da bikin ranar yaki da fataucin miyagun kwayoyi ta duniya a jihar.

Bayan kudurin Majalisar Dinkin Duniya (MDD) a shekarar 1987, ranar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi na duniya da nufin karfafa aiki da hadin gwiwa don cimma burin al’ummar duniya da ba ta su ga muggan kwayoyi.

  • Mutane 3 Sun Mutu A Hatsarin Mota, Biyu Sun Jikkata A Kogi
  • G7 Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Taimakon Ukraine A Yakinta Da Rasha

Bikin na 2022 mai taken cewa” Magance kalubalen shan kwayoyi a cikin Lafiya da Rikicin Jin kai yana da matukar dacewa dangane da cutar ta Korona da karuwar kalubalen tsaro a Nijeriya”.

 

A shekarar 2021, NDLEA ta kama sama da tan bakwai na haramtattun kwayoyi da kudinsu ya haura Naira Biliyan 130 tare da gurfanar da mutane sama da 900 da ake zargi.

Labarai Masu Nasaba

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

A nasa jawabin, Kwamandan NDLEA na shiyyar Sokoto, Kebbi da Zamfara, Muhammad Misbahu Idris, ya yabawa kokarin mai girma Sanata Abubakar Atiku Bagudu, da uwar gidansa Dakta Zainab Shinkafi Bagudu,  bisa gagarumin goyon baya da gudunmawar da suke bayarwa a Jihar Kebbi wajen ganin an magance matsalar na shan miyagun kwayoyi a fadin Jihar.

Haka kuma ya ce” yawaitar shaye-shayen miyagun kwayoyi a Nijeriya ya yi yawa, kafin yawan shan muggan kwayoyi a duniya ya kai kashi 15 cikin 100 amma a Nijeriya a yau ya kai kashi 15.

Haka zalika, ya yi kira ga iyaye da masu ruwa da tsaki da su zage damtse wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansu wajen kula da ‘ya’yansu da kyau don kaucewa ga fadawa cikin shan miyagun kwayoyi ko kuma abokantaka da Matasa masu shaye shaye.

Bugu da kari, ya yi kira ga jami’an hukumarsa da su kara kaimi wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansu na kamawa da gurfanar da masu aikata laifin shan miyagun kwayoyi.

Tun da farko, kwamishinan ma’aikatar kiwon lafiya na jihar, Jafar Muhammad, wanda ya wakilci gwamnan jihar Kebbi, ya yi alkawarin ci gaba da bayar da goyon bayan gwamnatin jihar domin dakile ta’ammali da miyagun kwayoyi a jihar.

A wani bangare na bikin rana, an gudanar da atisayen tafiya da kafa da rera wakoki daga ofishin jiha zuwa fadar Sarkin Gwandu, daga nan sai suka zarce zuwa masaukin fadar shugaban kasa, inda aka gudanar da lakcoci kan shaye-shayen miyagun kwayoyi da laifuka, da kuma haramcin shan miyagun kwayoyi a cikin al’umma.

Mahalarta taron, sun hada da sakatare na dindindin na Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kebbi, Wakilan Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa, Hukumar Kula da Lafiyar Jama’a ta Tarayya, Jami’an Hukumar Kare Hadura ta Kasa, Jami’an Tsaro da Tsaron Farar Hula, Kungiyoyin Sa-kai da Kungiyoyin Jama’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hukumar LafiyaKebbiKwamandaNDLEAShan Miyagun KwayoyiSokotoZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kafa Cibiyar Raya Al’Adu Da Tattalin Arzikin Sin Da Afrika A Fuzhou

Next Post

Dole Ne A Ci Gaba Da Binciken Alkalin Alkalai Mai Murabus, Tanko Muhammad — Majalisa

Related

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

6 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

9 hours ago
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo
Labarai

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

12 hours ago
Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet
Labarai

Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

14 hours ago
Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka
Manyan Labarai

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

15 hours ago
Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 
Manyan Labarai

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

19 hours ago
Next Post
Dole Ne A Ci Gaba Da Binciken Alkalin Alkalai Mai Murabus, Tanko Muhammad — Majalisa

Dole Ne A Ci Gaba Da Binciken Alkalin Alkalai Mai Murabus, Tanko Muhammad — Majalisa

LABARAI MASU NASABA

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.