ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

G7 Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Taimakon Ukraine A Yakinta Da Rasha

by Sadiq
4 years ago
Ukraine

Shugabannin kasashe bakwai masu karfin tattalin arzikin masana’antu a duniya (G7), sun lashi takobin ci gaba da marawa Ukraine baya dangane da mamayar da Rasha ta yi mata.

Cikin wata sanarwa da ta fitar yayin taronta a kudancin Jamus, G7 ta ce, za ta ci gaba da bai wa Ukraine tallafin kudi da na jin kai har da na soji da kuma na diflomasiyya tare da tsayawa kafa-da-kada da kasar da yaki ya daidaita.

  • An Gudanar Da Dandalin Cibiyoyin Ilimi Na Sin Da Afirka Na Shekarar 2022
  • NIS Ta Bi Ƙa’ida Sau Da Ƙafa Wajen Bai Wa David Nwamina Fasfo – CGI Isah Jere

Wannan sakon marawa Ukraine baya na zuwa ne bayan tattaunawar sama da sa’o’i biyu da shugabannin G7 suka yi da shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky, ta bidiyo.

ADVERTISEMENT

Shugaban Jamus mai masaukin baki Olaf Scholz, ta shafinsa na Twitter ya wallafa goyon bayan kungiyar na tsayawa kai da fata don taimaka wa Ukraine da tuni babban birninta Kiev ya fuskanci farmaki makami mai linzami daga Rasha.

Scholz, ya ce dole su dauki matakai masu tsauri da kuma suka dace, tare da kara matsin lamba kan Putin, don kawo karshen yakin.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Mambobin kungiyar sun gargadi Rasha kan bada damar jigilar kayayyakin abinci ficewa daga Ukraine domin kaucewa ta’azzara matsalar karancin abinci a duniya.

Shugabannin sun kuma yi kira ga Moscow da ta kyale ‘yan kasar Ukraine da aka tilastawa komawa gida nan take cikin aminci.

Kasashe masu arziki sun nuna matukar damuwarsu kan shirin da Rasha ke yi na isar da makamai masu linzami da za su iya daukar nukiliya zuwa Belarus a watanni masu zuwa.

Majiyar G7 ta ce, Zelensky ya bukaci shugabannin kasashen duniya da su yi iyakacin kokarinsu wajen ganin an kawo karshen mamayar da Rasha ke yi wa kasarsa a karshen wannan shekara, domin yanayin yaki zai kara tsanani ga dakarunsa yayin da suke kokarin kare kasarsu.

Zelensky ya jaddada bukatar ci gaba da daukar tsauraran matakai kan Rasha, da kuma kar a rage matsin lamba duk da takunkumin da kasashen yammacin Turai suka dauka kan Moscow.

Ya ce bai shirya bude tattaunawa da Rasha ba, saboda har yanzu Kyiv na neman karfafa matsayinta, in ji fadar shugaban kasar Faransa.

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Kotu Ta Yi Wa Wadanda Suka Kashe Wani Zabiya Daurin Rai Da Rai A Malawi

Kotu Ta Yi Wa Wadanda Suka Kashe Wani Zabiya Daurin Rai Da Rai A Malawi

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.