ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

G7 Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Taimakon Ukraine A Yakinta Da Rasha

by Sadiq
4 years ago
Ukraine

Shugabannin kasashe bakwai masu karfin tattalin arzikin masana’antu a duniya (G7), sun lashi takobin ci gaba da marawa Ukraine baya dangane da mamayar da Rasha ta yi mata.

Cikin wata sanarwa da ta fitar yayin taronta a kudancin Jamus, G7 ta ce, za ta ci gaba da bai wa Ukraine tallafin kudi da na jin kai har da na soji da kuma na diflomasiyya tare da tsayawa kafa-da-kada da kasar da yaki ya daidaita.

  • An Gudanar Da Dandalin Cibiyoyin Ilimi Na Sin Da Afirka Na Shekarar 2022
  • NIS Ta Bi Ƙa’ida Sau Da Ƙafa Wajen Bai Wa David Nwamina Fasfo – CGI Isah Jere

Wannan sakon marawa Ukraine baya na zuwa ne bayan tattaunawar sama da sa’o’i biyu da shugabannin G7 suka yi da shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky, ta bidiyo.

ADVERTISEMENT

Shugaban Jamus mai masaukin baki Olaf Scholz, ta shafinsa na Twitter ya wallafa goyon bayan kungiyar na tsayawa kai da fata don taimaka wa Ukraine da tuni babban birninta Kiev ya fuskanci farmaki makami mai linzami daga Rasha.

Scholz, ya ce dole su dauki matakai masu tsauri da kuma suka dace, tare da kara matsin lamba kan Putin, don kawo karshen yakin.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mambobin kungiyar sun gargadi Rasha kan bada damar jigilar kayayyakin abinci ficewa daga Ukraine domin kaucewa ta’azzara matsalar karancin abinci a duniya.

Shugabannin sun kuma yi kira ga Moscow da ta kyale ‘yan kasar Ukraine da aka tilastawa komawa gida nan take cikin aminci.

Kasashe masu arziki sun nuna matukar damuwarsu kan shirin da Rasha ke yi na isar da makamai masu linzami da za su iya daukar nukiliya zuwa Belarus a watanni masu zuwa.

Majiyar G7 ta ce, Zelensky ya bukaci shugabannin kasashen duniya da su yi iyakacin kokarinsu wajen ganin an kawo karshen mamayar da Rasha ke yi wa kasarsa a karshen wannan shekara, domin yanayin yaki zai kara tsanani ga dakarunsa yayin da suke kokarin kare kasarsu.

Zelensky ya jaddada bukatar ci gaba da daukar tsauraran matakai kan Rasha, da kuma kar a rage matsin lamba duk da takunkumin da kasashen yammacin Turai suka dauka kan Moscow.

Ya ce bai shirya bude tattaunawa da Rasha ba, saboda har yanzu Kyiv na neman karfafa matsayinta, in ji fadar shugaban kasar Faransa.

MASU ALAKA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
Labarai

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Kotu Ta Yi Wa Wadanda Suka Kashe Wani Zabiya Daurin Rai Da Rai A Malawi

Kotu Ta Yi Wa Wadanda Suka Kashe Wani Zabiya Daurin Rai Da Rai A Malawi

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.