• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NEF Ga Buhari: Kar Ka Sake A Karkashin Mulkinka Ka Bari IPOB Ta Hana ‘Yan NIjeriya Kada Kuri’a

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
NEF

Kungiyar dattawan Arewa (NEF) ta yi kira ga Shugaban kasa Muhammadu Buhari da kar ya sake a karkashin mulkinsa ya bari wata kungiya, musamman kungiyar neman kafa kasar Biafara (IPOB) ta hana ‘yan Nijeriya yin zabe.

A cikin sanarwar da mai magana da yawun kungiyar, Dakta Hakeem Baba-Ahmed ya fitar a ranar Talata, kungiyar ta yi Allah wadai da yadda IPOB ke barazana ga zaben 2023 a yankin kudu maso gabashin Nijeriya.

  • Za A Kira Taruka Biyu A Farkon Wata Mai Zuwa
  • Arewa An Sha Mu Mun Warke, Bai Kamata Mu Koma Gidan Jiya Ba – Matasan Arewa A Kudu

Kungiyar ta koka da yadda shuwagabanni, dattijai da ‘yan siyasa daga yankin da sauran sassan Nijeriya suka yi gum da bakunansu kan wannan barazana mai hatsari, wanda ta ce yana da matukar tayar da hankali.

Kungiyar ta jaddada cewa ‘yan NIjeriya na son a gudanar da sahihin zabe da kuma mika mulki cikin lumana zuwa gwamnati mai zuwa, inda ta ce babu wata kungiya da za a bari ta jefa al’ummar kasar cikin mawuyacin hali ta hanyar barazana ga zabe da zaman lafiya a kasar nan.

Ta ce: “Wadannan barazanar na biyo bayan hare-haren da ake kai wa gine-ginen gwamnati da kashe-kashe, ciki har da kashe ‘yansanda a yankin. Idan har ba a dauki matakan da suka dace ba, wadanda ke gudanar da ayyukan rashin bin doka suna iya dauka cewa za su yi nasara.

LABARAI MASU NASABA

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

“Duk wani yunkuri na yin katsalandan a ‘yancin ‘yan Nijeriya na shiga hurumin hana su zaben shugabanninsu, babban hari ne ga diyaucin Nijeriya kuma matakin da ya kamata a bijire masa ne.”

A cewar kungiyar, barazana ga zabuka babbar barazana ce ga tsarin dimokuradiyya da kuma ginshikin da al’ummar kasar suka dogara a kai, inda ta kara da cewa, idan har ta samu nasara, barazanar za ta nuna cewa za a fara wasu rikice-rikicen da kasar za ta kasa farfadowa.

“Kungiyar tana kira ga gwamnatin Shugaba Buhari da ta tabbatar da halaccin ikonta a kan duk wata kungiyar da ba ta da doka a kowane sashe na kasar nan tare da tabbatar da cewa ba a hana masu kada kuri’a ko barazana ba.”

Haka kuma, ta lura cewa dole ne shugabanni su fito fili su yi Allah wadai da wannan munanan barazanar tare da tabbatar wa ‘yan kasa masu kada kuri’a cewa za su iya yin hakan. Ta bayyana cewa dole ne ‘yan siyasa masu son shugabanci su fito su yi Allah wadai da wannan barazanar.

Ta ce don kauce wa shakku, barazanar da kungiyar da ke yankin kudu maso gabas ke yi na tsorata masu zabe, inda ta jaddada cewa wadanda ke bayansu su sani cewa za a yi musu tirjiya.

Kungiyar ta yi nuni da cewa so da yawa tana nanata matsayarta da kuma sauran kungiyoyin da ke kishin kasa masu muradin ganin an gudanar da zaben 2023 a duk fadin Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya
Tambarin Dimokuradiyya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 7, Sun Kwato Makamai A Kaduna 

Sojoji Sun Kashe 'Yan Bindiga 7, Sun Kwato Makamai A Kaduna 

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025
Asuu

An Janye Wajibcin Samun Kiredit A Darasin Lissafi Ga Ɗaliban Fannin Zamantakewa Don Shiga Manyan Makarantu 

October 14, 2025
Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.