• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NEF Ga Buhari: Kar Ka Sake A Karkashin Mulkinka Ka Bari IPOB Ta Hana ‘Yan NIjeriya Kada Kuri’a

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
NEF

Kungiyar dattawan Arewa (NEF) ta yi kira ga Shugaban kasa Muhammadu Buhari da kar ya sake a karkashin mulkinsa ya bari wata kungiya, musamman kungiyar neman kafa kasar Biafara (IPOB) ta hana ‘yan Nijeriya yin zabe.

A cikin sanarwar da mai magana da yawun kungiyar, Dakta Hakeem Baba-Ahmed ya fitar a ranar Talata, kungiyar ta yi Allah wadai da yadda IPOB ke barazana ga zaben 2023 a yankin kudu maso gabashin Nijeriya.

  • Za A Kira Taruka Biyu A Farkon Wata Mai Zuwa
  • Arewa An Sha Mu Mun Warke, Bai Kamata Mu Koma Gidan Jiya Ba – Matasan Arewa A Kudu

Kungiyar ta koka da yadda shuwagabanni, dattijai da ‘yan siyasa daga yankin da sauran sassan Nijeriya suka yi gum da bakunansu kan wannan barazana mai hatsari, wanda ta ce yana da matukar tayar da hankali.

Kungiyar ta jaddada cewa ‘yan NIjeriya na son a gudanar da sahihin zabe da kuma mika mulki cikin lumana zuwa gwamnati mai zuwa, inda ta ce babu wata kungiya da za a bari ta jefa al’ummar kasar cikin mawuyacin hali ta hanyar barazana ga zabe da zaman lafiya a kasar nan.

Ta ce: “Wadannan barazanar na biyo bayan hare-haren da ake kai wa gine-ginen gwamnati da kashe-kashe, ciki har da kashe ‘yansanda a yankin. Idan har ba a dauki matakan da suka dace ba, wadanda ke gudanar da ayyukan rashin bin doka suna iya dauka cewa za su yi nasara.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

“Duk wani yunkuri na yin katsalandan a ‘yancin ‘yan Nijeriya na shiga hurumin hana su zaben shugabanninsu, babban hari ne ga diyaucin Nijeriya kuma matakin da ya kamata a bijire masa ne.”

A cewar kungiyar, barazana ga zabuka babbar barazana ce ga tsarin dimokuradiyya da kuma ginshikin da al’ummar kasar suka dogara a kai, inda ta kara da cewa, idan har ta samu nasara, barazanar za ta nuna cewa za a fara wasu rikice-rikicen da kasar za ta kasa farfadowa.

“Kungiyar tana kira ga gwamnatin Shugaba Buhari da ta tabbatar da halaccin ikonta a kan duk wata kungiyar da ba ta da doka a kowane sashe na kasar nan tare da tabbatar da cewa ba a hana masu kada kuri’a ko barazana ba.”

Haka kuma, ta lura cewa dole ne shugabanni su fito fili su yi Allah wadai da wannan munanan barazanar tare da tabbatar wa ‘yan kasa masu kada kuri’a cewa za su iya yin hakan. Ta bayyana cewa dole ne ‘yan siyasa masu son shugabanci su fito su yi Allah wadai da wannan barazanar.

Ta ce don kauce wa shakku, barazanar da kungiyar da ke yankin kudu maso gabas ke yi na tsorata masu zabe, inda ta jaddada cewa wadanda ke bayansu su sani cewa za a yi musu tirjiya.

Kungiyar ta yi nuni da cewa so da yawa tana nanata matsayarta da kuma sauran kungiyoyin da ke kishin kasa masu muradin ganin an gudanar da zaben 2023 a duk fadin Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 7, Sun Kwato Makamai A Kaduna 

Sojoji Sun Kashe 'Yan Bindiga 7, Sun Kwato Makamai A Kaduna 

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.