• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NEF Ga Buhari: Kar Ka Sake A Karkashin Mulkinka Ka Bari IPOB Ta Hana ‘Yan NIjeriya Kada Kuri’a

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
NEF

Kungiyar dattawan Arewa (NEF) ta yi kira ga Shugaban kasa Muhammadu Buhari da kar ya sake a karkashin mulkinsa ya bari wata kungiya, musamman kungiyar neman kafa kasar Biafara (IPOB) ta hana ‘yan Nijeriya yin zabe.

A cikin sanarwar da mai magana da yawun kungiyar, Dakta Hakeem Baba-Ahmed ya fitar a ranar Talata, kungiyar ta yi Allah wadai da yadda IPOB ke barazana ga zaben 2023 a yankin kudu maso gabashin Nijeriya.

  • Za A Kira Taruka Biyu A Farkon Wata Mai Zuwa
  • Arewa An Sha Mu Mun Warke, Bai Kamata Mu Koma Gidan Jiya Ba – Matasan Arewa A Kudu

Kungiyar ta koka da yadda shuwagabanni, dattijai da ‘yan siyasa daga yankin da sauran sassan Nijeriya suka yi gum da bakunansu kan wannan barazana mai hatsari, wanda ta ce yana da matukar tayar da hankali.

Kungiyar ta jaddada cewa ‘yan NIjeriya na son a gudanar da sahihin zabe da kuma mika mulki cikin lumana zuwa gwamnati mai zuwa, inda ta ce babu wata kungiya da za a bari ta jefa al’ummar kasar cikin mawuyacin hali ta hanyar barazana ga zabe da zaman lafiya a kasar nan.

Ta ce: “Wadannan barazanar na biyo bayan hare-haren da ake kai wa gine-ginen gwamnati da kashe-kashe, ciki har da kashe ‘yansanda a yankin. Idan har ba a dauki matakan da suka dace ba, wadanda ke gudanar da ayyukan rashin bin doka suna iya dauka cewa za su yi nasara.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

“Duk wani yunkuri na yin katsalandan a ‘yancin ‘yan Nijeriya na shiga hurumin hana su zaben shugabanninsu, babban hari ne ga diyaucin Nijeriya kuma matakin da ya kamata a bijire masa ne.”

A cewar kungiyar, barazana ga zabuka babbar barazana ce ga tsarin dimokuradiyya da kuma ginshikin da al’ummar kasar suka dogara a kai, inda ta kara da cewa, idan har ta samu nasara, barazanar za ta nuna cewa za a fara wasu rikice-rikicen da kasar za ta kasa farfadowa.

“Kungiyar tana kira ga gwamnatin Shugaba Buhari da ta tabbatar da halaccin ikonta a kan duk wata kungiyar da ba ta da doka a kowane sashe na kasar nan tare da tabbatar da cewa ba a hana masu kada kuri’a ko barazana ba.”

Haka kuma, ta lura cewa dole ne shugabanni su fito fili su yi Allah wadai da wannan munanan barazanar tare da tabbatar wa ‘yan kasa masu kada kuri’a cewa za su iya yin hakan. Ta bayyana cewa dole ne ‘yan siyasa masu son shugabanci su fito su yi Allah wadai da wannan barazanar.

Ta ce don kauce wa shakku, barazanar da kungiyar da ke yankin kudu maso gabas ke yi na tsorata masu zabe, inda ta jaddada cewa wadanda ke bayansu su sani cewa za a yi musu tirjiya.

Kungiyar ta yi nuni da cewa so da yawa tana nanata matsayarta da kuma sauran kungiyoyin da ke kishin kasa masu muradin ganin an gudanar da zaben 2023 a duk fadin Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 7, Sun Kwato Makamai A Kaduna 

Sojoji Sun Kashe 'Yan Bindiga 7, Sun Kwato Makamai A Kaduna 

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.