• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nigeriya Da Tarayyar Turai Za Su Bunkasa Bincike Da Kirkire-kirkiren Fasaha

by Khalid Idris Doya
9 months ago
in Kimiyya Da Fasahar Sadarwa
0
Nigeriya Da Tarayyar Turai Za Su Bunkasa Bincike Da Kirkire-kirkiren Fasaha
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nijeriya da tarayyar Turai (EU) sun tsara dabarun hikimomi na yadda za su yi amfani da damarmakin kimiyya da fasahar zamani da kirkire-kirkire ta hanyar bincike da ci gaba, domin ganin an hada karfi da karfe wajen samar da ci gaba mai ma’ana.

Wannan batutuwan na daga cikin muhimman abubuwan da taron ganawa a tsakani, wanda ministan kere-keren kimiyya da fasaha, Uche Nnaji da tawagar EU wanda Ambasadansu a Nijeriya kuma na ECOWAS, Samuela Isopi ya wakilta da aka gudanar a Abuja.

  • Masu Zanga-zanga Sun Fito Duk Da Dokar Hana Fita A Jigawa
  • Rahoton Zanga-zangar YaÆ™i Da Fatara Da Tsadar Rayuwa A Nijeriya A Rana Ta 1

A jawabinsa, Nnaji ya ce kere-kere da bincike suna daga cikin manyan hanyoyin janyo ci gaba. Ya kara da cewa, ma’aikatar tasa ta himmatu wajen yin hadaka domin samar da hadin gwiwa da ganin an cimma nasarorin kai Nijeriya zuwa mataki na gaba.

Ya ce, “Ta hanyar kwarewa da kuma damarmakin abokan huldarmu wato Tarayyar Turai, za mu samu habaka ci gaban fasaharmu ta fuskacin da za mu iya shawo kan matsaloli da kalubalen da suke addabar yankunanmu. Bugu da kari, muna daukan matakin hadin gwiwa ta yadda za a kafa cibiyoyin kere-kere da kuma tallafa wa kanana da matsakaitan kamfanoninmu.”

Ya kara da cewa, zuba hannun jari a sashin bincike da ci gaba na matukar taimaka wa ci gaban tattalin arziki. Ya kuma kara da cewa, Nijeriya ta himmatu wajen ganin ta samar da yanayin da suka dace wajen cimma wannan nasarar.

Labarai Masu Nasaba

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

“Ma’aikatarmu ta maida hankali wajen inganta kwazo da horas da ma’aikatanmu ta fuskacni kyautata kwazonsu da kuma zurfafa bincike ta hanyar kyautata alakarmu da cibiyoyin bincike na Tarayyar Turai. Azamar da muka sanya kan makamashi da binciken kimiya za su taimaka sosai ga kasashen nan biyu, Nijeriya da abokan hulda Tarayyar Turai.

“Shirye-shiryen Erasmus da kan inganta ilimi da musayar bincike a tsakanin Nijeriya da Tarayyar Turai. Mun sanya azama wajen kara yawan ‘yan Nijeriya da za su halarci wannan shirye-shiryen kuma za mu tallafa musu wajen samun cike damar samun gurbi. Wannan zai taimaka mana wajen ganin mutanenmu da suke da hazaka sun samu damar fadada saninsu da kuma gogewarsu,” ya shaida.

Jagoran tawagar EU a Nijeriya, Isopi, a jawabinta, ta lura da cewa cimma yarjejeniyar da Nijeriya ta yi da EU kan fasahar kimiyya da kere-kere a matsayin wani babban matakin cimma nasara. Ta kara da cewa, lamarin kimiyya da fasaha muhimman bangarori ne wajen samar da ci gaba kamar su makamashi, noma da kuma wadata kasa da abinci.

Ta ce, tuni EU ta fara taimaka wa Nijeriya wajen bunkasa bincike da kere-kere, tare da karawa da cewa, wasu tulin damarmakin ma suna tafe domin kyautata harkokin kimiyya da fasaha a Nijeriya.

Ita kuma a nata bangaren, babbar sakatariya a ma’aikatar kere-kere da fasaha, Esuabana Nko-Asanye, ta roki EU ne da ta horas da jami’an Nijeriya masu aiki a bangaren kimiyya da fasaha domin inganta musu kwazonsu da saninsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FasahaNijeriyaTurkiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ƴansanda Sun Kama Mutane 64, Sun Ƙwato Buhun Taki 693 Daga Masu Zanga-zanga

Next Post

Zanga-Zanga Ba Ta Yi Tasiri A Rana Ta Uku Ba A Abuja

Related

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

4 weeks ago
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

2 months ago
Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet

2 months ago
Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet

3 months ago
Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani

7 months ago
Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk

7 months ago
Next Post
Zanga-Zanga Ba Ta Yi Tasiri A Rana Ta Uku Ba A Abuja

Zanga-Zanga Ba Ta Yi Tasiri A Rana Ta Uku Ba A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.