• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nigeriya Da Tarayyar Turai Za Su Bunkasa Bincike Da Kirkire-kirkiren Fasaha

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Kimiyya Da Fasahar Sadarwa
0
Nigeriya Da Tarayyar Turai Za Su Bunkasa Bincike Da Kirkire-kirkiren Fasaha
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nijeriya da tarayyar Turai (EU) sun tsara dabarun hikimomi na yadda za su yi amfani da damarmakin kimiyya da fasahar zamani da kirkire-kirkire ta hanyar bincike da ci gaba, domin ganin an hada karfi da karfe wajen samar da ci gaba mai ma’ana.

Wannan batutuwan na daga cikin muhimman abubuwan da taron ganawa a tsakani, wanda ministan kere-keren kimiyya da fasaha, Uche Nnaji da tawagar EU wanda Ambasadansu a Nijeriya kuma na ECOWAS, Samuela Isopi ya wakilta da aka gudanar a Abuja.

  • Masu Zanga-zanga Sun Fito Duk Da Dokar Hana Fita A Jigawa
  • Rahoton Zanga-zangar Yaƙi Da Fatara Da Tsadar Rayuwa A Nijeriya A Rana Ta 1

A jawabinsa, Nnaji ya ce kere-kere da bincike suna daga cikin manyan hanyoyin janyo ci gaba. Ya kara da cewa, ma’aikatar tasa ta himmatu wajen yin hadaka domin samar da hadin gwiwa da ganin an cimma nasarorin kai Nijeriya zuwa mataki na gaba.

Ya ce, “Ta hanyar kwarewa da kuma damarmakin abokan huldarmu wato Tarayyar Turai, za mu samu habaka ci gaban fasaharmu ta fuskacin da za mu iya shawo kan matsaloli da kalubalen da suke addabar yankunanmu. Bugu da kari, muna daukan matakin hadin gwiwa ta yadda za a kafa cibiyoyin kere-kere da kuma tallafa wa kanana da matsakaitan kamfanoninmu.”

Ya kara da cewa, zuba hannun jari a sashin bincike da ci gaba na matukar taimaka wa ci gaban tattalin arziki. Ya kuma kara da cewa, Nijeriya ta himmatu wajen ganin ta samar da yanayin da suka dace wajen cimma wannan nasarar.

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

“Ma’aikatarmu ta maida hankali wajen inganta kwazo da horas da ma’aikatanmu ta fuskacni kyautata kwazonsu da kuma zurfafa bincike ta hanyar kyautata alakarmu da cibiyoyin bincike na Tarayyar Turai. Azamar da muka sanya kan makamashi da binciken kimiya za su taimaka sosai ga kasashen nan biyu, Nijeriya da abokan hulda Tarayyar Turai.

“Shirye-shiryen Erasmus da kan inganta ilimi da musayar bincike a tsakanin Nijeriya da Tarayyar Turai. Mun sanya azama wajen kara yawan ‘yan Nijeriya da za su halarci wannan shirye-shiryen kuma za mu tallafa musu wajen samun cike damar samun gurbi. Wannan zai taimaka mana wajen ganin mutanenmu da suke da hazaka sun samu damar fadada saninsu da kuma gogewarsu,” ya shaida.

Jagoran tawagar EU a Nijeriya, Isopi, a jawabinta, ta lura da cewa cimma yarjejeniyar da Nijeriya ta yi da EU kan fasahar kimiyya da kere-kere a matsayin wani babban matakin cimma nasara. Ta kara da cewa, lamarin kimiyya da fasaha muhimman bangarori ne wajen samar da ci gaba kamar su makamashi, noma da kuma wadata kasa da abinci.

Ta ce, tuni EU ta fara taimaka wa Nijeriya wajen bunkasa bincike da kere-kere, tare da karawa da cewa, wasu tulin damarmakin ma suna tafe domin kyautata harkokin kimiyya da fasaha a Nijeriya.

Ita kuma a nata bangaren, babbar sakatariya a ma’aikatar kere-kere da fasaha, Esuabana Nko-Asanye, ta roki EU ne da ta horas da jami’an Nijeriya masu aiki a bangaren kimiyya da fasaha domin inganta musu kwazonsu da saninsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FasahaNijeriyaTurkiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ƴansanda Sun Kama Mutane 64, Sun Ƙwato Buhun Taki 693 Daga Masu Zanga-zanga

Next Post

Zanga-Zanga Ba Ta Yi Tasiri A Rana Ta Uku Ba A Abuja

Related

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

7 days ago
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

5 months ago
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

6 months ago
Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet

6 months ago
Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet

7 months ago
Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani

11 months ago
Next Post
Zanga-Zanga Ba Ta Yi Tasiri A Rana Ta Uku Ba A Abuja

Zanga-Zanga Ba Ta Yi Tasiri A Rana Ta Uku Ba A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

September 11, 2025
Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

September 11, 2025
Shettima

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

September 11, 2025
An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

September 11, 2025
Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Boko Haram Na Yin TikTok, Suna Sarrafa Jirage Marasa Matuƙi Don Sa Ido Kan Sansanonin Soji – Bulama 

Ƙwararren Masanin Tsaro, Bulama Ya Ƙaryata Iƙirarin El-Rufai Kan Biyan ’Yan Bindiga Kuɗaɗen Fansa

September 11, 2025
Wata Mahanga Ta Daban Na Kallon Ayyukan Ta’addanci

Wata Mahanga Ta Daban Na Kallon Ayyukan Ta’addanci

September 11, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.