ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nigeriya Da Tarayyar Turai Za Su Bunkasa Bincike Da Kirkire-kirkiren Fasaha

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Turai

Nijeriya da tarayyar Turai (EU) sun tsara dabarun hikimomi na yadda za su yi amfani da damarmakin kimiyya da fasahar zamani da kirkire-kirkire ta hanyar bincike da ci gaba, domin ganin an hada karfi da karfe wajen samar da ci gaba mai ma’ana.

Wannan batutuwan na daga cikin muhimman abubuwan da taron ganawa a tsakani, wanda ministan kere-keren kimiyya da fasaha, Uche Nnaji da tawagar EU wanda Ambasadansu a Nijeriya kuma na ECOWAS, Samuela Isopi ya wakilta da aka gudanar a Abuja.

  • Masu Zanga-zanga Sun Fito Duk Da Dokar Hana Fita A Jigawa
  • Rahoton Zanga-zangar Yaƙi Da Fatara Da Tsadar Rayuwa A Nijeriya A Rana Ta 1

A jawabinsa, Nnaji ya ce kere-kere da bincike suna daga cikin manyan hanyoyin janyo ci gaba. Ya kara da cewa, ma’aikatar tasa ta himmatu wajen yin hadaka domin samar da hadin gwiwa da ganin an cimma nasarorin kai Nijeriya zuwa mataki na gaba.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Ta hanyar kwarewa da kuma damarmakin abokan huldarmu wato Tarayyar Turai, za mu samu habaka ci gaban fasaharmu ta fuskacin da za mu iya shawo kan matsaloli da kalubalen da suke addabar yankunanmu. Bugu da kari, muna daukan matakin hadin gwiwa ta yadda za a kafa cibiyoyin kere-kere da kuma tallafa wa kanana da matsakaitan kamfanoninmu.”

Ya kara da cewa, zuba hannun jari a sashin bincike da ci gaba na matukar taimaka wa ci gaban tattalin arziki. Ya kuma kara da cewa, Nijeriya ta himmatu wajen ganin ta samar da yanayin da suka dace wajen cimma wannan nasarar.

LABARAI MASU NASABA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

“Ma’aikatarmu ta maida hankali wajen inganta kwazo da horas da ma’aikatanmu ta fuskacni kyautata kwazonsu da kuma zurfafa bincike ta hanyar kyautata alakarmu da cibiyoyin bincike na Tarayyar Turai. Azamar da muka sanya kan makamashi da binciken kimiya za su taimaka sosai ga kasashen nan biyu, Nijeriya da abokan hulda Tarayyar Turai.

“Shirye-shiryen Erasmus da kan inganta ilimi da musayar bincike a tsakanin Nijeriya da Tarayyar Turai. Mun sanya azama wajen kara yawan ‘yan Nijeriya da za su halarci wannan shirye-shiryen kuma za mu tallafa musu wajen samun cike damar samun gurbi. Wannan zai taimaka mana wajen ganin mutanenmu da suke da hazaka sun samu damar fadada saninsu da kuma gogewarsu,” ya shaida.

Jagoran tawagar EU a Nijeriya, Isopi, a jawabinta, ta lura da cewa cimma yarjejeniyar da Nijeriya ta yi da EU kan fasahar kimiyya da kere-kere a matsayin wani babban matakin cimma nasara. Ta kara da cewa, lamarin kimiyya da fasaha muhimman bangarori ne wajen samar da ci gaba kamar su makamashi, noma da kuma wadata kasa da abinci.

Ta ce, tuni EU ta fara taimaka wa Nijeriya wajen bunkasa bincike da kere-kere, tare da karawa da cewa, wasu tulin damarmakin ma suna tafe domin kyautata harkokin kimiyya da fasaha a Nijeriya.

Ita kuma a nata bangaren, babbar sakatariya a ma’aikatar kere-kere da fasaha, Esuabana Nko-Asanye, ta roki EU ne da ta horas da jami’an Nijeriya masu aiki a bangaren kimiyya da fasaha domin inganta musu kwazonsu da saninsu.

Turai
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

February 21, 2026
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Next Post
Zanga-Zanga Ba Ta Yi Tasiri A Rana Ta Uku Ba A Abuja

Zanga-Zanga Ba Ta Yi Tasiri A Rana Ta Uku Ba A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

September 11, 2026
Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

September 11, 2026
Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

September 11, 2026
Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

September 11, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

Dalilan Da Ya Sa Jam’iyyun Siyasa Suka Jinkirta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen

September 11, 2026
Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

September 11, 2026
Za A Ci ’Yan Siyasa Masu Kalaman Ɓatanci Tarar Miliyan 10 Da Ɗaurin Watanni 12 — INEC

2027: A Karon Farko INEC Za Ta Ƙaddamar Da Na’urar Bibiyar Zaɓen Nijeriya

September 11, 2026
Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

September 11, 2026
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026  Mrs Zubaida Umar

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026 Mrs Zubaida Umar

September 11, 2026
Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.