ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nigeriya Da Tarayyar Turai Za Su Bunkasa Bincike Da Kirkire-kirkiren Fasaha

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Turai

Nijeriya da tarayyar Turai (EU) sun tsara dabarun hikimomi na yadda za su yi amfani da damarmakin kimiyya da fasahar zamani da kirkire-kirkire ta hanyar bincike da ci gaba, domin ganin an hada karfi da karfe wajen samar da ci gaba mai ma’ana.

Wannan batutuwan na daga cikin muhimman abubuwan da taron ganawa a tsakani, wanda ministan kere-keren kimiyya da fasaha, Uche Nnaji da tawagar EU wanda Ambasadansu a Nijeriya kuma na ECOWAS, Samuela Isopi ya wakilta da aka gudanar a Abuja.

  • Masu Zanga-zanga Sun Fito Duk Da Dokar Hana Fita A Jigawa
  • Rahoton Zanga-zangar Yaƙi Da Fatara Da Tsadar Rayuwa A Nijeriya A Rana Ta 1

A jawabinsa, Nnaji ya ce kere-kere da bincike suna daga cikin manyan hanyoyin janyo ci gaba. Ya kara da cewa, ma’aikatar tasa ta himmatu wajen yin hadaka domin samar da hadin gwiwa da ganin an cimma nasarorin kai Nijeriya zuwa mataki na gaba.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Ta hanyar kwarewa da kuma damarmakin abokan huldarmu wato Tarayyar Turai, za mu samu habaka ci gaban fasaharmu ta fuskacin da za mu iya shawo kan matsaloli da kalubalen da suke addabar yankunanmu. Bugu da kari, muna daukan matakin hadin gwiwa ta yadda za a kafa cibiyoyin kere-kere da kuma tallafa wa kanana da matsakaitan kamfanoninmu.”

Ya kara da cewa, zuba hannun jari a sashin bincike da ci gaba na matukar taimaka wa ci gaban tattalin arziki. Ya kuma kara da cewa, Nijeriya ta himmatu wajen ganin ta samar da yanayin da suka dace wajen cimma wannan nasarar.

LABARAI MASU NASABA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

“Ma’aikatarmu ta maida hankali wajen inganta kwazo da horas da ma’aikatanmu ta fuskacni kyautata kwazonsu da kuma zurfafa bincike ta hanyar kyautata alakarmu da cibiyoyin bincike na Tarayyar Turai. Azamar da muka sanya kan makamashi da binciken kimiya za su taimaka sosai ga kasashen nan biyu, Nijeriya da abokan hulda Tarayyar Turai.

“Shirye-shiryen Erasmus da kan inganta ilimi da musayar bincike a tsakanin Nijeriya da Tarayyar Turai. Mun sanya azama wajen kara yawan ‘yan Nijeriya da za su halarci wannan shirye-shiryen kuma za mu tallafa musu wajen samun cike damar samun gurbi. Wannan zai taimaka mana wajen ganin mutanenmu da suke da hazaka sun samu damar fadada saninsu da kuma gogewarsu,” ya shaida.

Jagoran tawagar EU a Nijeriya, Isopi, a jawabinta, ta lura da cewa cimma yarjejeniyar da Nijeriya ta yi da EU kan fasahar kimiyya da kere-kere a matsayin wani babban matakin cimma nasara. Ta kara da cewa, lamarin kimiyya da fasaha muhimman bangarori ne wajen samar da ci gaba kamar su makamashi, noma da kuma wadata kasa da abinci.

Ta ce, tuni EU ta fara taimaka wa Nijeriya wajen bunkasa bincike da kere-kere, tare da karawa da cewa, wasu tulin damarmakin ma suna tafe domin kyautata harkokin kimiyya da fasaha a Nijeriya.

Ita kuma a nata bangaren, babbar sakatariya a ma’aikatar kere-kere da fasaha, Esuabana Nko-Asanye, ta roki EU ne da ta horas da jami’an Nijeriya masu aiki a bangaren kimiyya da fasaha domin inganta musu kwazonsu da saninsu.

Turai
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

February 21, 2026
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Next Post
Zanga-Zanga Ba Ta Yi Tasiri A Rana Ta Uku Ba A Abuja

Zanga-Zanga Ba Ta Yi Tasiri A Rana Ta Uku Ba A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026
Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark

Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark

July 13, 2026
Majalisar Gudanarwa Ta Sin Ta Wallafa “Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Karo Na 15 Kan Kiyaye Lafiyar Al’ummar Kasar”

Majalisar Gudanarwa Ta Sin Ta Wallafa “Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Karo Na 15 Kan Kiyaye Lafiyar Al’ummar Kasar”

July 13, 2026
Xi Zai Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026, Inda Zai Gabatar Da Muhimmin Jawabi

Xi Zai Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026, Inda Zai Gabatar Da Muhimmin Jawabi

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.