• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Da Brazil Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Bunkasa Tattalin Arziki

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
3 weeks ago
in Labarai
0
Nijeriya Da Brazil Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Bunkasa Tattalin Arziki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nijeriya da kasar Brazil sun sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna guda biyar domin inganta bangaren kasuwanci, diflomasiyya, kimiyya, sufurin jiragen sama da kuma hadin giwa a bangaren kudade.

Babban mashawarcin shugaban kasa kan yada labarai, Bayo Onanuga, shi ne ya sanar da wannan matakin a ranar Litinin. A cewarsa, Shugaban kasa Bola Tinubu ya yaba wa kokarin Shugaba Lula na sabunta kyakkyawar alaka a tsakanin kasashen biyu, ya nuna cewa har yanzu Nijeriya cike take da dimbin damarmakin da filayen da za su bai wa kamfanonin Brazil dama.

Shugaba Tinubu ya yi bayanin ziyarorin da ya kai kasar Brazil a baya wanda ya nuna gayar muhimmancin da ke akwai na kyautata alakar tattalin arziki a tsakanin kasashen.

Da yake fadada bayani kan bangarorin hadin gwiwar, Shugaba Tinubu ya nuna cewa Nijeriya a shirya take domin yin hadin giwa da kasar Brazil a bangaren musayar fasahohin zamani, wadata kasa da abinci, masana’antu, da kuma makamashi.

“Mun daukaka wannan alkawarin domin tabbatar da shi, kamar yadda kuka gani a cikin yarjejeniyar, ban san dalilin da ya sa masana’antar magunguna, wadanda Brazil ta yi zurfi da nisa a cikinsu ba za su iya kasancewa a Nijeriya ba.

Labarai Masu Nasaba

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

“Ban ga dalilin da ya sa ba a raba fifikon fasaha na Brazil da Afirka ba. Mun tabbatar wa junanmu cewa mune kawai za mu iya bunkasa tattalin arzikinmu don taimakawa kasarmu,” Tinubu ya shaida.

Tinubu ya kuma bai wa masu zuba hannun jari tabbacin cewa manufofin farfado da tattalin arzikin Nijeriya na haifar da sakamakon masu kyau a halin yanzu.

“Sauye-sauyen da na dukufa samarwa tun lokacin da na hau kan mulkin Nijeriya suna matukar tasiri. Da farko sun yi tsanani, amma a halin yanzu ana ganin gayar sakamakon masu kyau,” ya tabbatar.

Shi kuma a bangarensa, shugaba Lula na Brazil ya nuna farin cikinsa ne da sake sabunta kyakkyawar alaka tsakanin Nijeriya da Brazil. Ya ce, a halin yanzu da duniya ta ci gaba, akwai bangarori da daman gaske da kasashen biyu za su iya amfanar junansu.

Ya ce kasashen biyu suna da damarmaki sosai na fadaka a matsayinsu na manyan kasashen a duniya da bakaken fata suka fi yawa, za su iya amfanar junansu musamman ta bangarorin noma, kiwo, mai da gas, taki, jirgin sama, bangaren kanikanci da sauran bangarorin da dama.

Bayan tattaunawar ta tsawon awanni biyu, shugabannin kasashen biyu sun shaida sanya hannun fahimtar juna da aka yi a Palácio do Planalto da ke Brasília.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Ceto Mutum 117, Sun Kama Masu Laifi 150 Cikin Mako Guda

Next Post

Sin: Shawarar Gina Kyakkyawar Makomar Bil Adam Ta Bai Daya Ta Samu Amincewa A Duniya

Related

Brazil
Labarai

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

49 minutes ago
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 
Rahotonni

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

58 minutes ago
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma
Labarai

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

2 hours ago
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

2 hours ago
GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 19-09-2025

3 hours ago
Brazil
Labarai

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

4 hours ago
Next Post
Sin: Shawarar Gina Kyakkyawar Makomar Bil Adam Ta Bai Daya Ta Samu Amincewa A Duniya

Sin: Shawarar Gina Kyakkyawar Makomar Bil Adam Ta Bai Daya Ta Samu Amincewa A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Brazil

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

September 19, 2025
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

September 19, 2025
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

September 19, 2025

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

September 19, 2025
GORON JUMA’A 01-07-2025

GORON JUMA’A 19-09-2025

September 19, 2025
Brazil

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

September 19, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.