• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Fuskantar Karancin Kayan Noma

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Nijeriya Na Fuskantar Karancin Kayan Noma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Wasu jami’an gwamnati da na kamfanoni, sun bayyana sama da kashi 70 cikin dari na al’ummar kasar nan a matsayin wadanda suka dogara da fannin aikin noma, sai dai abin takaicin shi ne, Nijeriya na fuskantar kalubalen rashin wadatattun kayan aikin noma na zamani, wanda hakan ke jawo wa fannin aikin noman koma baya. 

Wata kididdiga da bankin duniya ya yi a kan harkar aikin noman a kasar nan, ya tabbatar da cewa; taraktocin da Nijeriya ta mallaka don yin noma bai haura 45,000 kacal ba, mai makon akalla guda 81,000 don aiwatar da harkokin noman.

  • Gwamna Uba Sani Ya Kafa Kwamitin Binciken Matsalolin Aiki Hajji
  • Basirar Henry Kissinger Abu Mai Daraja Ne Ga Amurka

Haka zalika, yanzu haka a kasar nan akwai akalla famfunan ban ruwan noman rani sama da 200,000 da sauran makamantansu.

Sannan, Nijeriya na da fadin kasar noma kuma ingantacciya kimanin 8,000, wanda hakan ke nuna cewa; kasar na da kimanin kadadar noma kimanin miliyan 80.

Bugu da kari, a cewar wani rahoton bankin duniya, bangaren gwamnati na shigo da akalla kashi 90 a cikin 100 na taraktocin noma cikin kasar nan, wanda kuma Ma’aikatar Aikin Noma da Raya Karkarar ce ke karbar wannan adadi, sannan mafi akasarinsu, kananan taraktoci ne.

Kazalika rahoton ya kara da cewa, bangaren kamfanoni masu zaman kansu, na shigo da taraktoci zuwa cikin kasar nan akalla kashi 10 cikin 100 a duk shekara.

Har ila yau, wadannan taraktocin noma na kai wa tsawon shekaru bakwai kafin su daina aiki, amma ya danganta da irin yadda samfurin taraktar ya ke.

Wakazalika, an kiyasta cewa sama da taraktocin noma 200 ne ke daina aiki duk da cewa, a duk shekara ana shigo da kimanin 1,000 Nijeriya.

Sai dai, domin kokarin lalubo mafita a kan karancin taraktocin, a kwanakin baya, Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci, ta kulla yarjejeniya da  kamfanin John Deere da ke kera taraktoci, domin samar da akalla taraktoci 2,000 ga wannan kasa, musamman domin a kara bunkasa fannin aikin noma na zamani.

Haka nan, ana sa ran wannan yarjejeniya da aka kulla; za ta kai tsawon shekaru biyar, wanda a karkashin yarjejeniyar za a samar wa Nijeriya taraktoci 10,000.

Ministan Aikin Noma da Samar da Abinci, Sanata Abubakar Kyari ya bayyana cewa, Nijeriya na fuskantar matukar karancin kayan aikin noma na zamani.

Kyari ya kara da cewa, ma’aikatarsa ta kulla yarjejeniya da kamfanin kera taraktoci na John Deere, domin samar da taraktoci sama da 2,000 a kan farashi mai sauki, don hakan ya bai wa kananan manoma samun damar siya a fadin wannan kasa baki-daya.

A cewar tasa, an samu damar kulla wannan yarjejeniya ce, biyo bayan wata ganawa a kwanakin baya da Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ya yi da wasu manyan jami’ai na Kamfanin John Deere a Kasar Amurka.

Wannan yarjejeniya, za ta kuma bai wa Kamfanin John Deere da abokan hadakar damar kafa masana’antar hada taraktoci a kasar nan, wadda bayan an sayi taraktocin; za kuma a dangana da su ga manoma kai tsaye.

Wakazalika, kwararru a fannin aikin noma a kasar nan, sun yi fatan dorewar wannan yarjejeniya, musamman ganin Ma’aikatar Aikin Noma a baya ta sha kulla ire-iren wannan yarjejeniya; amma sai ta gaza cimma burin da ta sanya a gaba.

Mista Jason Brantley, Mataimakin Shugaba a Kamfanin John Deere, ya bayyana jin dadinsa na shirin kafa kamfanin hada taraktocin noma a kasar nan.

Brantley ya sanar da cewa, kamfanin ya mayar da hankali ne wajen lalubo da mafita a kan kalubalen da kananan manoma ke fuskanta tare da habaka aikin noma da kayan aiki na zamani.

A cewarsa, Kamfanin John Deere ya mayar da hankali ne a kan yin noma da kayan aiki na zamani, domin aiwatar da aikin na noma mai tarin yawa a kadadar noma tare da kara bunkasa samar da wadataccen abinci a fadin kasar nan baki-daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Za Ta Samar Da Kundin Tattara Bayanai Na Ilimi

Next Post

Dusar Kankara Ta Sa An Dage Wasan Bayern Munich Da Union Berlin

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

2 weeks ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

2 weeks ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

4 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

4 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

1 month ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

1 month ago
Next Post
Dusar Kankara Ta Sa An Dage Wasan Bayern Munich Da Union Berlin

Dusar Kankara Ta Sa An Dage Wasan Bayern Munich Da Union Berlin

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe ÆŠan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe ÆŠan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin DaÉ—insa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.