ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Fuskantar Karancin Kayan Noma

by Abubakar Abba
3 years ago
Noma

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Wasu jami’an gwamnati da na kamfanoni, sun bayyana sama da kashi 70 cikin dari na al’ummar kasar nan a matsayin wadanda suka dogara da fannin aikin noma, sai dai abin takaicin shi ne, Nijeriya na fuskantar kalubalen rashin wadatattun kayan aikin noma na zamani, wanda hakan ke jawo wa fannin aikin noman koma baya. 

Wata kididdiga da bankin duniya ya yi a kan harkar aikin noman a kasar nan, ya tabbatar da cewa; taraktocin da Nijeriya ta mallaka don yin noma bai haura 45,000 kacal ba, mai makon akalla guda 81,000 don aiwatar da harkokin noman.

  • Gwamna Uba Sani Ya Kafa Kwamitin Binciken Matsalolin Aiki Hajji
  • Basirar Henry Kissinger Abu Mai Daraja Ne Ga Amurka

Haka zalika, yanzu haka a kasar nan akwai akalla famfunan ban ruwan noman rani sama da 200,000 da sauran makamantansu.

Sannan, Nijeriya na da fadin kasar noma kuma ingantacciya kimanin 8,000, wanda hakan ke nuna cewa; kasar na da kimanin kadadar noma kimanin miliyan 80.

Bugu da kari, a cewar wani rahoton bankin duniya, bangaren gwamnati na shigo da akalla kashi 90 a cikin 100 na taraktocin noma cikin kasar nan, wanda kuma Ma’aikatar Aikin Noma da Raya Karkarar ce ke karbar wannan adadi, sannan mafi akasarinsu, kananan taraktoci ne.

Kazalika rahoton ya kara da cewa, bangaren kamfanoni masu zaman kansu, na shigo da taraktoci zuwa cikin kasar nan akalla kashi 10 cikin 100 a duk shekara.

Har ila yau, wadannan taraktocin noma na kai wa tsawon shekaru bakwai kafin su daina aiki, amma ya danganta da irin yadda samfurin taraktar ya ke.

Wakazalika, an kiyasta cewa sama da taraktocin noma 200 ne ke daina aiki duk da cewa, a duk shekara ana shigo da kimanin 1,000 Nijeriya.

Sai dai, domin kokarin lalubo mafita a kan karancin taraktocin, a kwanakin baya, Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci, ta kulla yarjejeniya da  kamfanin John Deere da ke kera taraktoci, domin samar da akalla taraktoci 2,000 ga wannan kasa, musamman domin a kara bunkasa fannin aikin noma na zamani.

Haka nan, ana sa ran wannan yarjejeniya da aka kulla; za ta kai tsawon shekaru biyar, wanda a karkashin yarjejeniyar za a samar wa Nijeriya taraktoci 10,000.

Ministan Aikin Noma da Samar da Abinci, Sanata Abubakar Kyari ya bayyana cewa, Nijeriya na fuskantar matukar karancin kayan aikin noma na zamani.

Kyari ya kara da cewa, ma’aikatarsa ta kulla yarjejeniya da kamfanin kera taraktoci na John Deere, domin samar da taraktoci sama da 2,000 a kan farashi mai sauki, don hakan ya bai wa kananan manoma samun damar siya a fadin wannan kasa baki-daya.

A cewar tasa, an samu damar kulla wannan yarjejeniya ce, biyo bayan wata ganawa a kwanakin baya da Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ya yi da wasu manyan jami’ai na Kamfanin John Deere a Kasar Amurka.

Wannan yarjejeniya, za ta kuma bai wa Kamfanin John Deere da abokan hadakar damar kafa masana’antar hada taraktoci a kasar nan, wadda bayan an sayi taraktocin; za kuma a dangana da su ga manoma kai tsaye.

Wakazalika, kwararru a fannin aikin noma a kasar nan, sun yi fatan dorewar wannan yarjejeniya, musamman ganin Ma’aikatar Aikin Noma a baya ta sha kulla ire-iren wannan yarjejeniya; amma sai ta gaza cimma burin da ta sanya a gaba.

Mista Jason Brantley, Mataimakin Shugaba a Kamfanin John Deere, ya bayyana jin dadinsa na shirin kafa kamfanin hada taraktocin noma a kasar nan.

Brantley ya sanar da cewa, kamfanin ya mayar da hankali ne wajen lalubo da mafita a kan kalubalen da kananan manoma ke fuskanta tare da habaka aikin noma da kayan aiki na zamani.

A cewarsa, Kamfanin John Deere ya mayar da hankali ne a kan yin noma da kayan aiki na zamani, domin aiwatar da aikin na noma mai tarin yawa a kadadar noma tare da kara bunkasa samar da wadataccen abinci a fadin kasar nan baki-daya.

Noma
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Dusar Kankara Ta Sa An Dage Wasan Bayern Munich Da Union Berlin

Dusar Kankara Ta Sa An Dage Wasan Bayern Munich Da Union Berlin

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.