• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Karɓi Bashin Dala Biliyan 1.5 Daga Bankin Duniya Bayan Cire Tallafin Mai

by Khalid Idris Doya
4 months ago
in Manyan Labarai
0
Nijeriya Ta Karɓi Bashin Dala Biliyan 1.5 Daga Bankin Duniya Bayan Cire Tallafin Mai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bankin Duniya ta mika dala biliyan 1.5 a matsayin rancen waje ga Nijeriya a cikin yunkurin gwamnatin tarayya na aiwatar da cire tallafin man fetur da kuma yin kwaskwarima ga dokar haraji.

Wannan na kunshe ne a bayanin rancen da Bankin Duniyar ya fitar a baya-bayan nan.

Rancen wanda zai taimaka wajen farfado da tattalin arziki da aiwatar da manufofin kyautata harkokin kudi a cikin watanni shida.

  • Gwamna Fintiri Ya Nada Sabbin Sarakuna 7 A Jihar Adamawa
  • Bayan Cire Tallafin Mai Da Gyaran Dokar Haraji, Bankin Duniya Ya Danƙa Wa Nijeriya Bashi

Bayanin bankin ya nuna cewa an amince da bashin ne a ranar 3 ga watan Yunin 2024, kuma an sake kason farko na dala miliyan 750 a ranar 2 ga watan Yulin 2024, yayin da kuma aka turo wa Nijeriya sauran kudin a watan Disamba.

Kudin na dala biliyan 1.5 an bai wa Nijeriya da tsarin biya a lokuta daban-daban da nufin taimakawa wajen gudanar da ayyukan da za su farfado da tattalin arziki.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

Rancen farko na dala miliyan 750 da aka samu daga kungiyar ci gaban kasa da kasa na da tsawon shekaru 12 domin a biya. Yayin da kuma rance na biyun wato na dala miliyan 750 shi kuma za a biya shi a cikin shekaru 24 masu zuwa.

A cewar Bankin Duniyan, rancen da ta bai wa Nijeriya za ta taimaka wajen aiwatar da manufofin da za su kai ga farfadowa daga cire tallafin mai da daidaita musayar canjin kudi da kuma manufofin haraji.

Idan za a tuna dai a watan Oktoban 2024, gwamnatin tarayya ta mika kudirin gyara dokar haraji ga majalisar dokoki na kasa domin neman amincewa, wanda dokar ta janyo cece-kuce a tsakanin ‘yan Nijeriya, musamman shugabannin Arewa da suke zargin dokar ka iya janyo musu nakasu.

“An kuma aiwatar da garambawul don daidaita kasuwar man fetur gabaki daya, tare da tabbatar da cewa an kayyade farashin kayayyaki bisa yanayin kasuwa da bude fannin gasa. Hukumomin suna bin diddigin alkawarin da suka yi na dakatar da kasafin kudi tare da dogaro da daidaitattun kayan bashi don samar da givin.”

A halin da ake ciki, a cikin watannin da suka gabata, tsarin tagwayen manufofin gwamnati na cire da tallafin man fetur da hadewar musayar kudade ya jawo yabo, yayin da wasu kuma suka yi ta yir da su.

Musamman, a karkashin manufofin, farashin man fetur ya karu sau biyar, kuma farashin canji ya karu, wanda ya janyo tsadar rayuwa ga yawancin ‘yan Nijeriya.

Ko da yake gwamnatin tarayya ta vullo da hanyoyin yayyafa ruwa ga matsalar, kamar bayar da naira 25,000 ga gidaje, wanda gidaje miliyan biyu suka amfana, aiwatar da shirin amfani da motoci masu amfani da iskar gas, wanda shi ne mafi arha a kan mai don rage tasirin cire tallafin mai.

Lamarin ya janyo har tasirin hauhawar farashin kayan abinci, ya haura zuwa kashi 34.60 da kashi 39.93, bi da bi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Banki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Ta Jaddada Aniyarta Ta Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Yammacin Afirka

Next Post

ACF Ta Nemi Rundunar Soji Ta Sake Dabarun Yakinta, Bayan Luguden Wutar Silame

Related

Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

4 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

7 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

8 hours ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

16 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

22 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

1 day ago
Next Post
ACF Ta Nemi Rundunar Soji Ta Sake Dabarun Yakinta, Bayan Luguden Wutar Silame

ACF Ta Nemi Rundunar Soji Ta Sake Dabarun Yakinta, Bayan Luguden Wutar Silame

LABARAI MASU NASABA

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.