ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Karɓi Bashin Dala Biliyan 1.5 Daga Bankin Duniya Bayan Cire Tallafin Mai

by Khalid Idris Doya
12 months ago
Nijeriya

Bankin Duniya ta mika dala biliyan 1.5 a matsayin rancen waje ga Nijeriya a cikin yunkurin gwamnatin tarayya na aiwatar da cire tallafin man fetur da kuma yin kwaskwarima ga dokar haraji.

Wannan na kunshe ne a bayanin rancen da Bankin Duniyar ya fitar a baya-bayan nan.

Rancen wanda zai taimaka wajen farfado da tattalin arziki da aiwatar da manufofin kyautata harkokin kudi a cikin watanni shida.

ADVERTISEMENT
  • Gwamna Fintiri Ya Nada Sabbin Sarakuna 7 A Jihar Adamawa
  • Bayan Cire Tallafin Mai Da Gyaran Dokar Haraji, Bankin Duniya Ya Danƙa Wa Nijeriya Bashi

Bayanin bankin ya nuna cewa an amince da bashin ne a ranar 3 ga watan Yunin 2024, kuma an sake kason farko na dala miliyan 750 a ranar 2 ga watan Yulin 2024, yayin da kuma aka turo wa Nijeriya sauran kudin a watan Disamba.

Kudin na dala biliyan 1.5 an bai wa Nijeriya da tsarin biya a lokuta daban-daban da nufin taimakawa wajen gudanar da ayyukan da za su farfado da tattalin arziki.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Rancen farko na dala miliyan 750 da aka samu daga kungiyar ci gaban kasa da kasa na da tsawon shekaru 12 domin a biya. Yayin da kuma rance na biyun wato na dala miliyan 750 shi kuma za a biya shi a cikin shekaru 24 masu zuwa.

A cewar Bankin Duniyan, rancen da ta bai wa Nijeriya za ta taimaka wajen aiwatar da manufofin da za su kai ga farfadowa daga cire tallafin mai da daidaita musayar canjin kudi da kuma manufofin haraji.

Idan za a tuna dai a watan Oktoban 2024, gwamnatin tarayya ta mika kudirin gyara dokar haraji ga majalisar dokoki na kasa domin neman amincewa, wanda dokar ta janyo cece-kuce a tsakanin ‘yan Nijeriya, musamman shugabannin Arewa da suke zargin dokar ka iya janyo musu nakasu.

“An kuma aiwatar da garambawul don daidaita kasuwar man fetur gabaki daya, tare da tabbatar da cewa an kayyade farashin kayayyaki bisa yanayin kasuwa da bude fannin gasa. Hukumomin suna bin diddigin alkawarin da suka yi na dakatar da kasafin kudi tare da dogaro da daidaitattun kayan bashi don samar da givin.”

A halin da ake ciki, a cikin watannin da suka gabata, tsarin tagwayen manufofin gwamnati na cire da tallafin man fetur da hadewar musayar kudade ya jawo yabo, yayin da wasu kuma suka yi ta yir da su.

Musamman, a karkashin manufofin, farashin man fetur ya karu sau biyar, kuma farashin canji ya karu, wanda ya janyo tsadar rayuwa ga yawancin ‘yan Nijeriya.

Ko da yake gwamnatin tarayya ta vullo da hanyoyin yayyafa ruwa ga matsalar, kamar bayar da naira 25,000 ga gidaje, wanda gidaje miliyan biyu suka amfana, aiwatar da shirin amfani da motoci masu amfani da iskar gas, wanda shi ne mafi arha a kan mai don rage tasirin cire tallafin mai.

Lamarin ya janyo har tasirin hauhawar farashin kayan abinci, ya haura zuwa kashi 34.60 da kashi 39.93, bi da bi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
ACF Ta Nemi Rundunar Soji Ta Sake Dabarun Yakinta, Bayan Luguden Wutar Silame

ACF Ta Nemi Rundunar Soji Ta Sake Dabarun Yakinta, Bayan Luguden Wutar Silame

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.