• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Tafka Asarar Dala Biliyan 1.5 Sakamakon Watsi Da Fannin Kiwon Dabbobi

by Abubakar Abba
10 months ago
in Labarai
0
Nijeriya Ta Tafka Asarar Dala Biliyan 1.5 Sakamakon Watsi Da Fannin Kiwon Dabbobi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana takaicinsa na watsi da ka yi da fannin kiwon dabbobi a Nijeriya, wanda hakan ya yi sanadiyyar karancin samar da Madarar Shanu da ake fitarwa zuwa kasashen waje tare da tafka asarar kudin shiga har kimanin dala biliyan 1.5.

Kazalika, shugaban ya yi nuni da cewa, “Lokaci ya yi da ya kamata mu yi abin da ya dace, musamman idan aka yi la’akari da cewa; wannan kasa na dauke da al’umma sama da miliyan 200, don haka bai kamata a gaza shayar da ‘ya’yanmu Madara ba; a lokacin da suke daukar darussa a Ajujuwansu na karatu a kullum ba”.

  • Dalilan Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Rungumar Sabuwar Dabarar Kiwo A Kano
  • Yadda Masu Kiwon ‘Yan Tsakin Gidan Gona Ke Ganin Tasku A Kano

Ya bayyana hakan ne, a kwanakin baya lokacin da ya kaddamar da bunkasa shirin farfado da kiwon dabbobi na kasa.

Idan za a iya tunawa, shirin na bunkasa kiwon dabbobin; Shugaba Tinubu ne ya kirkiro da shi, inda kuma ya kafa kwamitin samar da sabon sauyi a fannin a ranar 19 ga watan Yulin 2024, kafin ya kirkiro da masana’antar da za ta sanya ido ga fannin na kiwon dabbobin.

Ya kara da cewa, “Fannin kiwon, abu ne da ke da matukar muhimmanci, kuma za mu ba shi dukkanin kulawar da ta dace, musamman domin dawo da kimar wannan kasa tamu.”

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Da yake yin karin haske a kan muhimmancin da fannin ke da shi a wannan kasa, shugaban ya sanar da cewa; ana bukatar litar Madara akalla tan biliyan 0.7.

Ya ci gaba da cewa, ana kuma bukatar tan biliyan 1.48 na Nama da Kwai; shi ma kimanin tan miliyan 1.48, inda ya sanar da cewa; sai dai abin takaicin shi ne, ba a iya samar da wadannan adadi.

Shugaban ya kara da cewa, yawan litar da ake amfani da ita na Madarar, ta kai kimanin 8.7; wacce ta yi daidai da kilo 9 na Nama, sai kuma kilo 3.5 na Kwai da ya kai kimanin kilo 45.

Har ila yau, ya bayar da tabbacin cewa; Nijeriya za ta iya cimma burin da ta sanya a gaba na sake farfado da fannin kiwon dabbobin, duba da cewa fannin na kara habaka tattalin arzikin wannan kasa tare kuma da samar da ayyukan yi ga ‘yan Nijeriya.

Ya kuma sanar da cewa, akwai damammaki da dama da muke iya gani da idanuwanmu, inda ya sanar da cewa; za mu tabbatar da ganin mun samar da kyakkyawan yanayi, musamman domin kasuwancin fannin ya tumbatsa a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kiwo
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilin Da Ya Sa Farashin Wake Ba Zai Sauka Ba A Nijeriya -Masana

Next Post

’Yan Bindiga Sun Sace ’Yan Uwan Ɗan Jarida a Kogi, Sun Nemi Fansar Naira Miliyan 50

Related

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Labarai

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

5 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

6 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

7 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

10 hours ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

11 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

11 hours ago
Next Post
’Yan Bindiga Sun Sace ’Yan Uwan Ɗan Jarida a Kogi, Sun Nemi Fansar Naira Miliyan 50

’Yan Bindiga Sun Sace ’Yan Uwan Ɗan Jarida a Kogi, Sun Nemi Fansar Naira Miliyan 50

LABARAI MASU NASABA

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.