ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 29, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Tafka Asarar Dala Biliyan 1.5 Sakamakon Watsi Da Fannin Kiwon Dabbobi

by Abubakar Abba
2 years ago
Kiwo

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana takaicinsa na watsi da ka yi da fannin kiwon dabbobi a Nijeriya, wanda hakan ya yi sanadiyyar karancin samar da Madarar Shanu da ake fitarwa zuwa kasashen waje tare da tafka asarar kudin shiga har kimanin dala biliyan 1.5.

Kazalika, shugaban ya yi nuni da cewa, “Lokaci ya yi da ya kamata mu yi abin da ya dace, musamman idan aka yi la’akari da cewa; wannan kasa na dauke da al’umma sama da miliyan 200, don haka bai kamata a gaza shayar da ‘ya’yanmu Madara ba; a lokacin da suke daukar darussa a Ajujuwansu na karatu a kullum ba”.

  • Dalilan Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Rungumar Sabuwar Dabarar Kiwo A Kano
  • Yadda Masu Kiwon ‘Yan Tsakin Gidan Gona Ke Ganin Tasku A Kano

Ya bayyana hakan ne, a kwanakin baya lokacin da ya kaddamar da bunkasa shirin farfado da kiwon dabbobi na kasa.

ADVERTISEMENT

Idan za a iya tunawa, shirin na bunkasa kiwon dabbobin; Shugaba Tinubu ne ya kirkiro da shi, inda kuma ya kafa kwamitin samar da sabon sauyi a fannin a ranar 19 ga watan Yulin 2024, kafin ya kirkiro da masana’antar da za ta sanya ido ga fannin na kiwon dabbobin.

Ya kara da cewa, “Fannin kiwon, abu ne da ke da matukar muhimmanci, kuma za mu ba shi dukkanin kulawar da ta dace, musamman domin dawo da kimar wannan kasa tamu.”

LABARAI MASU NASABA

Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

Da yake yin karin haske a kan muhimmancin da fannin ke da shi a wannan kasa, shugaban ya sanar da cewa; ana bukatar litar Madara akalla tan biliyan 0.7.

Ya ci gaba da cewa, ana kuma bukatar tan biliyan 1.48 na Nama da Kwai; shi ma kimanin tan miliyan 1.48, inda ya sanar da cewa; sai dai abin takaicin shi ne, ba a iya samar da wadannan adadi.

Shugaban ya kara da cewa, yawan litar da ake amfani da ita na Madarar, ta kai kimanin 8.7; wacce ta yi daidai da kilo 9 na Nama, sai kuma kilo 3.5 na Kwai da ya kai kimanin kilo 45.

Har ila yau, ya bayar da tabbacin cewa; Nijeriya za ta iya cimma burin da ta sanya a gaba na sake farfado da fannin kiwon dabbobin, duba da cewa fannin na kara habaka tattalin arzikin wannan kasa tare kuma da samar da ayyukan yi ga ‘yan Nijeriya.

Ya kuma sanar da cewa, akwai damammaki da dama da muke iya gani da idanuwanmu, inda ya sanar da cewa; za mu tabbatar da ganin mun samar da kyakkyawan yanayi, musamman domin kasuwancin fannin ya tumbatsa a Nijeriya.

Kiwo
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ku Gaggauta Fara Yin Shuka A Kakar Bana: Saƙon Hukumar NiMet Ga Manoma
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos

MASU ALAKA

Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina
Labarai

Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina

June 29, 2026
Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha
Manyan Labarai

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

June 28, 2026
An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja
Manyan Labarai

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

June 28, 2026
Next Post
’Yan Bindiga Sun Sace ’Yan Uwan Ɗan Jarida a Kogi, Sun Nemi Fansar Naira Miliyan 50

’Yan Bindiga Sun Sace ’Yan Uwan Ɗan Jarida a Kogi, Sun Nemi Fansar Naira Miliyan 50

LABARAI MASU NASABA

Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina

Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina

June 29, 2026
Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

June 28, 2026
Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

June 28, 2026
An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

June 28, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

June 28, 2026
Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

June 28, 2026
Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

June 28, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.