ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Masu Kiwon ‘Yan Tsakin Gidan Gona Ke Ganin Tasku A Kano

by Abubakar Abba and Sulaiman
2 years ago
Kiwo

A yayin da Nijeriya ke ci gaba da fusknatar kalubalen tattalin arziki da kuma hauhawar farashin kaya, wanda aka ruwaito cewa; shi ne mafi kamari a cikin shekaru 17 da suka wuce, hakan ya kuma shafi masu sana’ar kiwon kajin gidan gona, inda wasu masu sana’ar a Jihar Kano; tsadar ‘yan tsakin da abincinsu ta tilasata su dakatar da sana’ar.

 

Wani daga cikin masu sana’ar a jihar, Bala Idris ya sanar da cewa; tuni wasu daga cikinsu suka durkushe, sakamakon wannan matsala; inda wasu kuma da dama ke ci gaba da fafutukar lalubo mafita dangane da wannan kalubale da fannin ke fuskanta a jihar.

ADVERTISEMENT
  • Rikicin PDP: A Daina Maganar Tsayawa Takarar Shugaban Kasa A 2027, A Maida Hankali Kan Jam’iyya –Saraki
  • Mutfwang Ya Amince Da Mafi Karancin Albashi Na N70,000 Ga Ma’aikatan Filato

Wasu masu sana’ar kuma su ma sun bayyana cewa, farashin abincin kaji da kuma na ‘yan tsakin; ya fi tashi a cikin watan Nuwamba zuwa watan Disamba, amma a cikin wannan shekarar; tashin farashin ya fi yin kamari matuka, sabanin shekarun baya.

 

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Wasu masu ruwa da tsaki a fannin da ke a jihar, Yakubu Ibrahim; wanda ke da gonar kiwon kajin da ake kira ‘Albarka’ ya sanar da cewa, saboda kalubalen biyu a yanzu, baya iya gudanar da aikin kamar a baya, inda ya kara da cewa; a baya ba su taba fuskantar irin wannan kalubale ba.

 

Ibrahim ya ce, akwai abubuwa da dama da suka jawo hakan wadanda suka hada da tsadar kajin da abincinsu, inda hakan ya jawo wasu ke barin ko ficewa daga sana’ar.

 

Ya kara da cewa, ana kuma fuskantar kalubalen masu yin kyankyasar ‘yan tsaki a jihar, inda ya kara da cewa; daukacin ‘yan tsakin ana shigo da su ne daga kudancin kasar nan, domin akasari ba a cika samun kamfanonin da ke yin kyankyasar ‘yan tsakin a jihar ba.

 

Ibrahim ya kara da cewa, masu kiwon kajin da ake kira da ‘Broilers’ a turance a jihar, su ne suka fi fuskantar wannan kalubale; domin farashinsu ya tashi matuka, wanda kuma ba a taba ganin hakan a baya ba.

 

A cewarsa, akasarin hakan ya fi afkuwa a lokacin bukukuwan karshen shekara da kuma lokacin gudanar da bikin Kirismeti, domin masu kiwon suna ci gaba da kiwon nasu ne har tsawon wata uku ko hudu kafin ‘yan tsakin su girma.

 

“Masu kiwon kaji da ake kira ‘Broilers’ a turance a jihar, su ne suka fi fuskantar wannan kalubale; domin farashinsu ya tashi matuka wanda kuma ba a taba ganin hakan a baya ba”.

 

Bincike ya nuna cewa, a yanzu haka ana kara samun bukatar kajin, inda hakan kuma ya shafi rabar da kajin a yankunan Arewa.

 

A yanzu dai, ana sayar da ‘yan tsakin kyankyasar kwana daya a kan Naira 800, inda kuma ba a iya sayen ‘yan tsakin da aka kyankyashe a cikin sati biyu ganin cewa kowane daya ana sayarwa a kan Naira 1,000; kuma babu wanda zai yarda ya sayi kowane daya a kan Naira 2,000.

 

Shi ma wani mai ruwa da tsaki a fannin, Mansur Shehu Kiru; mai gonar kiwon kajin da ake kira da ‘Rahama Agro’ ya bayyana cewa, ya rage yawan kajin daga 2,000 zuwa 400, sakamakon tsadar safararsu daga garin Ibadan zuwa Kano.

 

Ya ci gaba da cewa, magungunan kajin ma sun yi tashin gwauron zabi, inda ya kara da cewa; wannan ma babban kalubale ne da masu sana’ar ke fusktanta a jihar.

 

Ya ce, a ‘yan tsakin na ‘broiler’ a shekarar da ta wuce, ana sayar da duk guda daya a kan Naira 500; amma yanzu farashin ya kai daga Naira 800 zuwa Naira 850.

 

Mansur Shehu, a baya ana sayar da buhun abincin ‘yan tsakin a kan Naira 3,500, amma yanzu farshin ya kai daga Naira 8,000 zuwa Naira 9,000.

 

Shi ma wani mai ruwa da tsaki a fannin, Zaharaddin Yakasai; wanda ke da gonar kiwon da ake kira da ‘Yaks’ a Jihar Kano ya sanar da cewa, abincin kajin ya yi matukar tsada a bana, musamman saboda matsin tattalin arzikin da kasar nan ke fuskanta.

 

Zaharaddin Yakasai ya bayyana cewa, saboda wadannan kalubale wasu masu sana’r suka dakatar da ita, domin tafiyar da fannin a halin yanzu; akwai matukar wahala.

 

Ya sanar da cewa, idan ka lissafa za ka ga ba wata ribar kirki muke samu ba, inda ya ce; wasu na barin sana’ar wasu kuma sun rage yawan adadin wadanda suke kiwatawa.

 

A cewar Zaharaddin Yakasai, muna matukar bukatar gwamnati ta kawo mana dauki, musamman ganin yadda fannin ke taimakawa wajen samar da ayyukan yi na kai tsaye da kuma wadanda ba na kai tsaye ba a jihar, musamman a tsakanin matasan jihar.

 

Zaharaddin Yakasai, ya kuma koka a kan yadda duk da wadannan kalubale da masu sana’ar ke ci gaba da fuskanta, amma masu karbar haraji tun daga kananan hukomomi har zuwa matakin jiha; ba sa daga musu kafa, inda ya sanar da cewa; masu karbar harajin na karbar daga Naira 100,000 zuwa Naira 300,000.

 

“Akwai matukar bukatar gwamnati ta kawo mana dauki, musamman ganin yadda fannin ke taimakawa wajen samar da ayyukan yi kai tsaye da kuma wadanda ba na kai tsaye ba a jihar, musamman a tsakanin matasa”.

 

Shi ma, wani dilan ‘yan tsaki da sauran tsintsaye a jihar; Abdurrahman Suleiman Tarauni ya bayyana cewa, sana’ar a halin yanzu ba ta tafiya yadda ya kamata, inda ya kara da cewa; a yanzu ana sayar da abincin kajin daga Naira 8,000 zuwa Naira 9,000, inda hakan ya sa mutane ba sa iya saya.

Kiwo
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
Kiwo
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Dawanau

Abin Da Ya Sa Masu Saye Da Sayar Da Amfanin Gona A Kaduna Suka Ragu

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.