• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NiMet Ta Yi Hasashen Samun Hadari Da Tsawa Na Kwanaki 3 Daga Ranar Litinin

by Sadiq
3 years ago
NiMet

Hukumar kula da yanayi ta Nijeriya, NiMet, ta yi hasashen samun hadari, tsawa da kuma mamakon ruwan sama daga ranar Litinin zuwa Laraba a fadin kasar nan.

Hasashen yanayin na NiMet da aka fitar a ranar Lahadi a Abuja, ya yi hasashen sararin samaniya a ranar Litinin da tazarar hasken rana a yankin Arewa da safiya.

  • Kwankwaso Ba Zai Yi Wa Peter Obi Takarar Mataimaki Ba — NNPP
  • Farashin Gas Din Girki Ya Kara Yin Tashin Gwauron Zabi — NBS

A cewarta, ana sa ran samun tsawa a sassan jihohin Taraba, Bauchi, Borno, Yobe, Adamawa, Gombe, Kaduna, Kano, Jigawa, Katsina, Zamfara da Sakkwato a cikin sa’o’i da rana.

Hukumar ta yi hasashen yanayi na gajimare a yankin Arewa ta tsakiya da safe.

An yi hasashen za a yi tsawa a wasu sassan Kogi, Kwara, Filato, Benue, Neja da kuma babban birnin tarayya Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

NiMet ta yi hasashen yiwuwar samun ruwan sama a jihohin Cross River, Rivers da Bayelsa.

Ta kuma yi hasashen samun tsawa a jihohin Enugu, Ondo, Edo, Imo da Anambra da yammacin ranar Litinin tare da yiwuwar samun ruwan sama a jihohin Akwa Ibom, Delta, Cross River, Rivers da Bayelsa.

“A ranar Talata ana sa ran za a yi tsawa a sassan jihohin Borno, Adamawa, Taraba, Bauchi, Jigawa, Yobe, Gombe da Kaduna. Ana sa ran iska mai karfi za ta ke kadawa tare da tsawa musamman jihohin Borno da Yobe da kuma Jigawa.

“A washegari, ana sa ran za a yi tsawa a sassan jihohin Kano, Katsina, Kaduna, Zamfara, Kebbi da Sakkwato.

Hukumar ta yi hasashen yiwuwar samun tsawa a wasu sassan Filato, Kogi, Nasarawa, Neja da kuma babban birnin tarayya.

An yi hasashen za a samu ruwan sama a jihohin Enugu, Ogun, Ondo, Edo, Bayelsa, Rivers, Cross River da kuma Legas da rana da yamma.

“A ranar Laraba, ana sa ran za a yi tsawa a sassan jihohin Taraba, Bauchi, Borno, Gombe, Kaduna, Kano, Jigawa, Katsina, Zamfara da Sakkwato da safe.

“A washegari, akwai yiwuwar tsawa a wasu sassan jihohin Yobe da Adamawa.

“Ana sa ran samun hadari a yankin da yiwuwar yin tsawa a sassan Nasarawa, Kwara da kuma Babban Birnin Tarayya da safe.

“An shawarci ma’aikatan jirgin sama da su samu sabbin rahotannin yanayi daga NiMet don inganta yanayin ayyukansu,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
Labarai

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Next Post
Gwamnatin Kaduna Ta Sake Sallamar Malaman Makaranta 2,357 Daga Aiki

Gwamnatin Kaduna Ta Sake Sallamar Malaman Makaranta 2,357 Daga Aiki

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.