ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NiMet Ta Yi Hasashen Samun Hadari Da Tsawa Na Kwanaki 3 Daga Ranar Litinin

by Sadiq
4 years ago
NiMet

Hukumar kula da yanayi ta Nijeriya, NiMet, ta yi hasashen samun hadari, tsawa da kuma mamakon ruwan sama daga ranar Litinin zuwa Laraba a fadin kasar nan.

Hasashen yanayin na NiMet da aka fitar a ranar Lahadi a Abuja, ya yi hasashen sararin samaniya a ranar Litinin da tazarar hasken rana a yankin Arewa da safiya.

  • Kwankwaso Ba Zai Yi Wa Peter Obi Takarar Mataimaki Ba — NNPP
  • Farashin Gas Din Girki Ya Kara Yin Tashin Gwauron Zabi — NBS

A cewarta, ana sa ran samun tsawa a sassan jihohin Taraba, Bauchi, Borno, Yobe, Adamawa, Gombe, Kaduna, Kano, Jigawa, Katsina, Zamfara da Sakkwato a cikin sa’o’i da rana.

ADVERTISEMENT

Hukumar ta yi hasashen yanayi na gajimare a yankin Arewa ta tsakiya da safe.

An yi hasashen za a yi tsawa a wasu sassan Kogi, Kwara, Filato, Benue, Neja da kuma babban birnin tarayya Abuja.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

NiMet ta yi hasashen yiwuwar samun ruwan sama a jihohin Cross River, Rivers da Bayelsa.

Ta kuma yi hasashen samun tsawa a jihohin Enugu, Ondo, Edo, Imo da Anambra da yammacin ranar Litinin tare da yiwuwar samun ruwan sama a jihohin Akwa Ibom, Delta, Cross River, Rivers da Bayelsa.

“A ranar Talata ana sa ran za a yi tsawa a sassan jihohin Borno, Adamawa, Taraba, Bauchi, Jigawa, Yobe, Gombe da Kaduna. Ana sa ran iska mai karfi za ta ke kadawa tare da tsawa musamman jihohin Borno da Yobe da kuma Jigawa.

“A washegari, ana sa ran za a yi tsawa a sassan jihohin Kano, Katsina, Kaduna, Zamfara, Kebbi da Sakkwato.

Hukumar ta yi hasashen yiwuwar samun tsawa a wasu sassan Filato, Kogi, Nasarawa, Neja da kuma babban birnin tarayya.

An yi hasashen za a samu ruwan sama a jihohin Enugu, Ogun, Ondo, Edo, Bayelsa, Rivers, Cross River da kuma Legas da rana da yamma.

“A ranar Laraba, ana sa ran za a yi tsawa a sassan jihohin Taraba, Bauchi, Borno, Gombe, Kaduna, Kano, Jigawa, Katsina, Zamfara da Sakkwato da safe.

“A washegari, akwai yiwuwar tsawa a wasu sassan jihohin Yobe da Adamawa.

“Ana sa ran samun hadari a yankin da yiwuwar yin tsawa a sassan Nasarawa, Kwara da kuma Babban Birnin Tarayya da safe.

“An shawarci ma’aikatan jirgin sama da su samu sabbin rahotannin yanayi daga NiMet don inganta yanayin ayyukansu,” in ji shi.

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Gwamnatin Kaduna Ta Sake Sallamar Malaman Makaranta 2,357 Daga Aiki

Gwamnatin Kaduna Ta Sake Sallamar Malaman Makaranta 2,357 Daga Aiki

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.