Hukumar kula da yanayi ta ƙasa (NiMet), ta yi hasashen samun ruwan sama mai yawa, sannan da yiwuwar ambaliya a wasu sassa na Nijeriya daga Litinin zuwa Laraba.
Jihohin Arewa kamar Kano, Kaduna, Katsina, Jigawa da Bauchi na iya fuskantar ambaliya.
- An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025
- Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
A Arewa ta Tsakiya kuma, Abuja, Filato da Nasarawa za su fuskanci ruwan sama.mai ƙarfi.
A Kudu kuwa, ana sa ran samum ruwan sama mai ƙarfi a jihohin Ribas, Kuros Riba, Delta da Akwa Ibom.
NiMet ta shawarci jama’a da su guji tuƙi a lokacin da ake yin ruwan sama mai ƙarfi, su zauna cikin gida.
Sannan su É—aure kayan da iska za iya É—auka.
Ta kuma shawarci kamfanonin jiragen sama da su nemi rahoton yanayi kafin tashi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp