• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS: ACG James Sunday Ya Kai Ziyarar Inganta Aiki Maiduguri

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
NIS: ACG James Sunday Ya Kai Ziyarar Inganta Aiki Maiduguri
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mataimakin Kwanturola Janar na Hukumar Shige da Fice ta Kasa (NIS), ACG James Sunday, ya ziyarci kwamandan rundunar Operation Hadin Kai a hedikwatar hukumar da ke Arewa maso Gabas a Maiduguri a karkashin jagorancin Manjo Janar W Shaibu domin tattauna gudunmawar da hukumar za ta bai wa rundunar a Maiduguri.

Taron ya samu halartar Babban Kwanturolan hukumar reshen Jihar Borno, CIS Abba Salihu da mataimakansa da ke shiyyar C, Manjo Janar W Shaibu da sauran manyan hafsoshin soji da ke hadin gwiwa da rundunar.

  • Kannywood Wuri Ne Na Nishadi Ba Gyaran Tarbiyya Ba -Fauziyya D Suleiman
  • Abubuwan Da Za Su Taimaka Wa Mai Azumi Ya Kasance Cikin Koshin Lafiya

Ko’odinetan Shiyyar C (Arewa maso Gabas), wadda ta kunshi jihohin Adamawa, Bauchi, Borno, Gombe, Yobe da Filato bayan sun ziyarci jihar Yobe, ya ziyarce su ne domin tantance ayyukan rundunar tare da jadadda umarnin sake bude iyakar Nijeriya da Jamhuriyar Nijar, sannan zai dawo Maiduguri domin ci gaba da ziyarar aikin kwanaki biyu a jihohin Borno da Yobe.

Haka zalika hukumar ta umarci rundundar da ke Jihar Borno da ta sake bude iyakar Nijeriya ci gaba da zirga-zirgar mutane zuwa Nijeriya da da sauran al’amuran yau da kullum kamar da yadda aka saba a baya.

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa tana da jami’ai da maza kusan 230 da aka tura zuwa rundunar hadin gwiwa, domin kyautata dangantakar ta aiki da hadin kai.

Labarai Masu Nasaba

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

A cewar Kwamandan, jami’an NIS sun kware sosai wajen aikinsu dangane da shige da fice da sauransu. Jami’an sun samu horo da tsarin aiki karkashin jagorancin Manjo Janar W Shaibu kamar yadda aka bayyana a yayin taron.

“Ni da kaina na taso daga Maiduguri zuwa Damaturu domin tantance yanayin aikin da ake yi”, in ji ACG James.

“Ina tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa an samu kwanciyar hankali da tsaro a yankin Arewa maso Gabas, harkokin tattalin arziki da na cikin gida sun dawo a jihohin Barno da Yobe, motoci suna zirga-zirga cikin lafiya tare da kayayyaki zuwa sassan kasar nan.

“Ina mika godiya ga dukkan jami’an da ke kan hanyar da sojoji ke aiki ba dare ba rana a kewayen tafkin Chadi da kan iyaka, wannan namijin kokari ne kuma abun a yaba ne, in ji shi.

“Ina son jinjina wa jami’ain NIS tare da mika godiyata a gare su.”

Gwamnatin Jihar Borno ta za ta shirya wani babban taron tsaro a Maiduguri, bisa tsarin NIS a yankin Arewa Maso Gabas, don samar da hanyoyin da za a tabbatar da tsaro da zaman lafiya a yankin a kamar yadda mataimakin gwamnan jihar, Umar Usman Kadafur ya bayyana a lokacin da ya ziyarci ofishin hukumar na shiyyar C, da ke gidan gwamnatin jihar a Maiduguri.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kannywood Wuri Ne Na Nishadi Ba Gyaran Tarbiyya Ba -Fauziyya D Suleiman

Next Post

Wasannin Afirka 2024: Ko Ghana Za Ta Iya Abin Arziki?

Related

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara
Labarai

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

2 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

3 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

3 hours ago
Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri
Labarai

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

6 hours ago
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

7 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

8 hours ago
Next Post
Wasannin Afirka 2024: Ko Ghana Za Ta Iya Abin Arziki?

Wasannin Afirka 2024: Ko Ghana Za Ta Iya Abin Arziki?

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

September 14, 2025
An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

September 14, 2025
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

September 14, 2025
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

September 14, 2025
Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

September 14, 2025
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.