• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Na Saukaka Samun Fasfo A Ribas, Ta Samar Da Fasfo 6,000 A Wata Guda

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
NIS Na Saukaka Samun Fasfo A Ribas, Ta Samar Da Fasfo 6,000 A Wata Guda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kula da shige da fice ta kasa (NIS) reshen jihar Ribas ta himmatu wajen fito da tsare-tsaren da suke saukakawa da shawo kan matsalolin da ake samu na jinkirin samar da fasfo domin kauce wa matsin lamba na bukatar fasfon.

NIS a karkashin jagorancin CIS James Sunday a jihar ta Ribas ta samar da littafin fasfot har guda 6,000 a cikin wata daya tak da ya taimaka sosai wajen rage tulin bukatun fasfo da jama’a ke gabatawa da kuma saukaka samar wa mutane da fasfo din.

Sabon jami’in kula da harkokin fasfo, mai mukamim mataimakin Kwanturola, Audi Musa Maisudan sa’ilin da ke bayani wa Kwanturolan hukumar na jihar, James Sunday a lokacin ziyarar aiki zuwa ofishin aikin fasfo da ke Mile 1 a garin Fatakwal, ya ce, sabon tsarin ya rage jinkirin da ake samu wajen samar wa jama’a da fasfon a lokacin da suka bukata.

  • Magoya Bayan PDP Sun Yi Zanga-Zanga Dauke Da Kayan Tsafi A Ribas

 

A nasa bangaren, Kwanturola James Sunday, ya jinjina wa sabon jami’in tare da tawagarsa bisa himmar da suka nuna wajen biyayya ga umarnin ministan harkokin cikin gida Ogbeni Rauf Aregbesola da Kwanturol Janar na hukumar NIS, CGI Isah Jere Idris na cewa kada a bari samar wa jama’a da Fasfo ya zama abun damuwa ko wahala ga ‘yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

Murabus ÆŠin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin ÆŠaukar Wani Mataki

Ya ce, umarnin ya taimaka matuka wajen saukaka hanyoyin da ake bi wajen samar da fasfon ta yadda ake biya wa masu bukatun fasfot din bukatun su ba tare da wani tarnaki ba.

A cewarsa, “Tsarin ya taimaka wajen rage koma baya da shan wahala, kuma duk mai bukata da ya bi ka’ida yana samun fasfo din sa a ranakun da aka gindaya wanda ya rage caza kwakwalwa, da kawo saukin aiki.”

“Na kawo ziyarar ce domin gani da idona kan ko an bi umarnin Minista da Kwanturola Janar, kuma na gamsu da yadda na ga Jami’ai sun dukufa wajen inganta aiki. Kuma dole ne a mutunta jama’a a samar musu da fasfo kan lokaci kuma bisa sauki ba tare da sai sun sha wahala ba.

“Mun kuma kwashi tsoffin hannu wadanda suka jima mun sauya musu sashi illa iyaka kwararrun da ake da bukatar aikinsu matuka, yin hakan zai ba da dama wadanda suka dace kuma suke da karsashin aikin su ne za su rika tafiyar da lamuran domin saukaka samar da fasfo ga jama’a.”

Daga bisani ya gargadi masu sako-sako da aiki ko kauce wa ka’idar aiki su shiga taitayinsu domin hukumar ta NIS ba za ta lamunci sakaci da aiki ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AikiFasfonNIS
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Fitar Da Rahoton Farko Game Da Cika Shekaru 10 Da Kaddamar Da Shawarar Kafa Al’umma Mai Makomar Bai Daya Ga Dukkanin Bil Adama

Next Post

A Ci Gaba Da Wanzar Da Ruhin Mazan Jiya, In Ji Xi Jinping

Related

Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

6 minutes ago
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba
Labarai

Murabus ÆŠin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin ÆŠaukar Wani Mataki

1 hour ago
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

4 hours ago
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

13 hours ago
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu
Labarai

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

15 hours ago
Zaben 2027 YaÆ™i Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 YaÆ™i Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

19 hours ago
Next Post
A Ci Gaba Da Wanzar Da Ruhin Mazan Jiya, In Ji Xi Jinping

A Ci Gaba Da Wanzar Da Ruhin Mazan Jiya, In Ji Xi Jinping

LABARAI MASU NASABA

Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Sin Ta Kalubalanci Kasashen Yammacin Duniya Da Su Tuna Da Laifinsu Na Mulkin Mallaka

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

June 30, 2025
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba

Murabus ÆŠin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin ÆŠaukar Wani Mataki

June 30, 2025
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.