• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Ribas Ta Bukaci Mutunta Umarnin Bangaren Zartarwa Kan Aikin Yi Ga ‘Yan Kasa

by yahuzajere
2 years ago
NIS

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), reshen Jihar Ribas ta nanata bukatar kamfanoni da kungiyoyi su mutunta Dokar Bangaren Zartarwa kan ayyukan Injiniya don bai wa ‘yan Nijeriya isassun ayyukan yi ta yadda za a tabbatar da cewa wadanda ba ‘yan Nijeriya ba, ba su shiga ayyukan da aka san akwai kwararrun ‘yan Nijeriya da za su iya gudanarwa ba.

A cewar NIS, Dokar mai taken ‘Executive Order Five’ da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sanya wa hannu a shekarar 2018, ta kudiri aniyar bunkasa kimiyya, fasahar kere-kere da kuma shigar da kamfanonin cikin gida a ayyukan gwamnati da suka hada da daben zamani na Tiling da Interlocks da jera bulolluka na gini da dai sauransu wadanda aka tabbatar da cewa ‘yan kasa za su iya yin aiki mai kyau kuma daidai wajen gudanar da su.

A wata tattaunawa da Kwanturolan Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa reshen Jihar Ribas, CIS James Sunday, ranar Alhamis, a yayin da rundunar take shirin gudanar da taron kwana daya da masu ruwa da tsaki da kamfanonin da suka amince da bayar da kaso na ‘yan kasashen ketare, ya bayyana cewa NIS ta dukufa wajen tabbatar da ganin ana bin ka’ida a bangaren bayar da izinin kasuwanci da kuma daukar ma’aikata da sauran harkokin zuba jari da suke da nasaba da hukumar tasu ta shige da fice.

Sama da kamfanoni dari ne ake sa ran za su halarci taron bitar na yini guda a garin Fatakwal na jihar Ribas.

NIS

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

Ya kuma yi nuni da cewa, dole ne a takaita wuraren da ‘yan kasar waje ke aiki da aka tabbatar akwai ‘yan Nijeriya da za su iya yi kamar yadda Dokar Zartaswa a bangaren aikin Injiniya ta tanada kuma a ba su cikakkiyar dama ba tare da wata shakka ba don sanya ‘yan Nijeriya su ci gajiyar wuraren aiki a Nijeriya, ta yadda za a rage masu sha’awar fita waje neman aikin musamman matasa masu neman aikin yi domin bunkasa walwalar rayuwarsu.

…Manyan Kalubalen Da Sabbin Shugabannin Majalisa Za Su Iya Fuskanta

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC
Manyan Labarai

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
Next Post
Mukaddashiyar Shugabar NIS Ta Ayyana Dokar Ta-baci Kan Ayyukan Fasfo

Mukaddashiyar Shugabar NIS Ta Ayyana Dokar Ta-baci Kan Ayyukan Fasfo

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.