• Leadership Hausa
Tuesday, June 28, 2022
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

NIS Ta Buɗe Cibiyar Fasfo Ta Zamani Da Za Ta Karaɗe Jihohin Edo Da Delta

by yahuzajere
5 days ago
in Labarai
0
Fasfo

Daga dama: Kwanturolar NIS ta Edo, Rabi Garba, Gwamna Obaseki na Edo, Minista Aregbesola, Shugaban NIS CGI ISah Idris Jere da ACG Domnic Asogwa yayin bude cibiyar ta fasfo

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ta ƙaddamar da cibiyar bayar da ingataccen fasfo na zamani da za ta karaɗe jihohin Edo da Delta.

Hukumar ta ƙaddamar da cibiyar ce a ranar Talatar nan bisa jagorancin Ministan Cikin Gida Rauf Ogbeni Aregbesola da Shugaban NIS, CGI Isah Idris Jere.

Fasfo
CGI Isah Idris yayin da aka tarbe shi a Benin yayin kaddamarwar

Sanarwar da Jami’in hulɗa da jama’a na NIS, ACI Amos Okpu ya fitar, ta bayyana cewa, da yake ƙaddamar da cibiyar, Minista Aregbesola ya ce cibiyar za ta dinga biyan buƙatun masu neman fasfo da suka fito daga yankunan jihohin Edo da Delta.

Ministan ya ƙara da cewa, cibiyar za ta kasance ta musamman da za ta kula da ofishoshin fasfo na jihohin guda biyu, saboda ƙara inganta ayyukan samar da fasfo a waɗannan jihohi.

  • Tawagar NIS Ta Kai Ziyarar Aiki A Poland Kan Tsaron Iyakoki

Ya ƙara da cewa bisa ƙaddamar da cibiyar, ofisoshin fasfo na jihohin Edo da Delta za su yi aiki kafaɗa da kafaɗa da sauran wurare da ke yankin kudu maso gabas da kudu maso yamma wajen samun nasarar bunƙasa ɓangaran fasfo na zamani.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Aka Tilastawa Tsohon Alkalin-alkalai Tanko Yin Murabus Din Dole

Majalisar Dokokin Zamfara Ta Amince Da Dokar Hukunta ‘Yan Bindiga Da Sauran Laifuffuka

Fasfo
CGI Isah Idris Jere (na farko a dama) da sauran manyan baki a fadar Oba na Benin

Minstan ya ce inganta fasfo na zamani wata dama ce da masu buƙatar za su zaɓi nau’in fasfo da suke muradi, kamar mai feji 32 da ke aiki na tsawon shekaru biyar da mai feji 64 da ke aiki na tsawon shekaru biyar da kuma mai feji 64 da ke aiki na tsawon shekaru 10.

Ya ce inganta harkokin fasfo zuwa na zamani hanya ce ta ƙara bunƙasa fasaha, musamman inganta sha’anin taro ta yadda kundayen hukumar da ke ɗauke da bayanai za su yi wahalar kwaikwayo da buga na jabu.

A cewarsa, an samar da wannan cibiya ce domin sauƙaƙa wa masu neman tare da kauce wa wahalar da su zuwa wuri main isa a duk lokacin da suka buƙaci samun fasfo, ta yadda za su yi amfani da na’urar zamani wajen gabatar da buƙatarsu ta samun fasfo cikin kwanciyar hanhali a gidajensu ko kuma a ofishinsu.

Fasfo
Minista Aregbesola yayin da yake kaddamar da ofishin fasfon

Ministan ya jaddada cewa gwamnati tana ƙara wasu shirye-shirye wajen tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya suna samun fasfo cikin sauƙi ba tare da wata wahala ba.

A nasa jawabin, Kwanturola Janar na Hukumar NIS, Isah Jere Idris ya bayyana cewa samar da cibiyar ingantaccen fasfo na zamani da ke Benin na ɗaya daga cikin ƙoƙarin sauye-sauyen da yake aiwatarwa a ɓangaren, musamman wajen ƙara faɗaɗa wa masu neman fasfo hanyoyin samu da kuma zaɓi a kan irin wanda suke muradi.

Ya buƙaci masu neman fasfo da su ziyarci shafin hukumar na intanet a passport.immigration.gov.ng a kowani lokaci, domin biyan kuɗaɗe da kuma gabatar da buƙatar neman fasfo tun kafin lokaci ya ƙure, domin kaucewa cunkoso lokacin da suke buƙata.

Ya ƙara da cewa hukumar ba ta amince da biyan tsabar kuɗi ba, inda ya yi kira da masu nema da su tabbatar sun biya kuɗaɗensu ta shafin intanet tun kafin su ziyarci ofisoshin fasfo lokacin da aka tsara musu.

Tun da farko dai, Gwamnan Jihar Edo, Mista Godwin Noheghase Obaseki ya yaba wa hukumar NIS bisa samar da waɗannan sauye-sauye wajen bayar da fasfo. Ya nuna jin daɗinsa wajen zaɓar garin Benin a matsayin cibiya ta wannan aiki, inda ya sha alwashin cewa gwamnatinsa za ta bayar da duk wata gudummuwa da hukumar take buƙata ciki har da tabbacin goyon bayan ƙudurin aikin gina ofishin fasfo a Auchi.

Fasfo
Minista Aregbesola yana jawabi a fadar Oba na Benin

Bugu da ƙari, Sarkin Benin, Mai Martaba Omo no’ Oba n’Edo Uku Akpolokpolo, Oba Ewuare II, Ogidigan ya yaba wa Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari bisa amincewa da kafa cibiyar ingantaccen fasfon na zamani a masarautarsa. Ya ƙara da cewa shugaban ƙasa ya daɗe yana faranta wa mutanen Jihar Edo rai da kuma ‘yan Nijeriya gaba ɗaya.

Ya tabbatar da cewa zai bayar da goyon baya kan wannan aiki tare da miƙa godiyarsa ga Ministan Harkokin Cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola bisa jagorantar manyan jami’an hukumar NIS da kuma sauran ma’aikatu da suka zo yankinsa.

  • https://passport.immigration.gov.ng/

A cikin waɗanda suka halarci ƙaddamar da katafariyar cibiyar ta fasfo har da Hon. Justice PA Akhikhero wanda ya wakilci Alƙalin-alƙalai na jihar, da shugaban ma’aikatan gwamna da muƙaddashin shugaban jami’ar Ambrose Alli, Farfesa Osarheme Osadolor, da shugabannin rundunar sojojin Nijeriya da sauran jami’an tsaro.

 

 

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ina Jin Takaici Da Damuwa Kan Yadda Ake Fita Daga Jam’iyyarmu Ta APC —Abdullahi Adamu

Next Post

Al’umar Mai’adua Na Bukatar Gyaran Masallacin Juma’arsu Da Ya Shafe Shekaru Ba Gyara

Related

Zargin Cin Hanci: Alkalin Alkalai, Tanko Muhammad Ya Ajiye Mukaminsa
Labarai

Yadda Aka Tilastawa Tsohon Alkalin-alkalai Tanko Yin Murabus Din Dole

51 mins ago
Dalilan Da Ya Sa Muka Halatta Sayen Bindiga Don Kare Kai —Gwamnatin Zamfara
Labarai

Majalisar Dokokin Zamfara Ta Amince Da Dokar Hukunta ‘Yan Bindiga Da Sauran Laifuffuka

2 hours ago
Alaramma Sadeeq Umar Da Ya Wakilci Nijeriya A Musabakar Al-qur’ani Ta Tanzaniya Ya Rasu
Rahotonni

Alaramma Sadeeq Umar Da Ya Wakilci Nijeriya A Musabakar Al-qur’ani Ta Tanzaniya Ya Rasu

11 hours ago
2023: INEC Ta Kara Wa’adin Yin Rajistar Katin Zabe
Labarai

2023: INEC Ta Kara Wa’adin Yin Rajistar Katin Zabe

12 hours ago
Dubun Wadanda Suka Kwakwule Idon Wani Yaro A Bauchi Ta Cika
Al'ajabi

Dubun Wadanda Suka Kwakwule Idon Wani Yaro A Bauchi Ta Cika

13 hours ago
An Kashe Kasurgumin Dan Fashin Dajin Da Ya Addabi Mutane A Leren Jihar Kaduna
Labarai

An Kashe Kasurgumin Dan Fashin Dajin Da Ya Addabi Mutane A Leren Jihar Kaduna

14 hours ago
Next Post
Al’umar Mai’adua Na Bukatar Gyaran Masallacin Juma’arsu Da Ya Shafe Shekaru Ba Gyara

Al'umar Mai'adua Na Bukatar Gyaran Masallacin Juma'arsu Da Ya Shafe Shekaru Ba Gyara

LABARAI MASU NASABA

Zargin Cin Hanci: Alkalin Alkalai, Tanko Muhammad Ya Ajiye Mukaminsa

Yadda Aka Tilastawa Tsohon Alkalin-alkalai Tanko Yin Murabus Din Dole

June 28, 2022
Dalilan Da Ya Sa Muka Halatta Sayen Bindiga Don Kare Kai —Gwamnatin Zamfara

Majalisar Dokokin Zamfara Ta Amince Da Dokar Hukunta ‘Yan Bindiga Da Sauran Laifuffuka

June 28, 2022
Alaramma Sadeeq Umar Da Ya Wakilci Nijeriya A Musabakar Al-qur’ani Ta Tanzaniya Ya Rasu

Alaramma Sadeeq Umar Da Ya Wakilci Nijeriya A Musabakar Al-qur’ani Ta Tanzaniya Ya Rasu

June 27, 2022
2023: INEC Ta Kara Wa’adin Yin Rajistar Katin Zabe

2023: INEC Ta Kara Wa’adin Yin Rajistar Katin Zabe

June 27, 2022
An Gudanar Da Gasar Harshen Sinanci Ta Chinese Bridge Ga Daliban Jami’a Da Na Sakandare A Uganda

An Gudanar Da Gasar Harshen Sinanci Ta Chinese Bridge Ga Daliban Jami’a Da Na Sakandare A Uganda

June 27, 2022
Dubun Wadanda Suka Kwakwule Idon Wani Yaro A Bauchi Ta Cika

Dubun Wadanda Suka Kwakwule Idon Wani Yaro A Bauchi Ta Cika

June 27, 2022
Kasar Sin Za Ta Kara Zuba Jari A Fannin Muhallin Halittu

Kasar Sin Za Ta Kara Zuba Jari A Fannin Muhallin Halittu

June 27, 2022
An Kashe Kasurgumin Dan Fashin Dajin Da Ya Addabi Mutane A Leren Jihar Kaduna

An Kashe Kasurgumin Dan Fashin Dajin Da Ya Addabi Mutane A Leren Jihar Kaduna

June 27, 2022
Rikicin Kabilanci: An Fara Binciken Wasu Manyan Sarakuna A Kogi

Rikicin Kabilanci: An Fara Binciken Wasu Manyan Sarakuna A Kogi

June 27, 2022
Buhari Ya Rantsar Da Ariwoola A Matsayin Sabon Alkalin Alkalai Na Kasa

‘Yan Bindiga Sun Sace DPO A Kaduna

June 27, 2022
ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.