ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Buɗe Cibiyar Fasfo Ta Zamani Da Za Ta Karaɗe Jihohin Edo Da Delta

by yahuzajere
4 years ago
Fasfo

Daga dama: Kwanturolar NIS ta Edo, Rabi Garba, Gwamna Obaseki na Edo, Minista Aregbesola, Shugaban NIS CGI ISah Idris Jere da ACG Domnic Asogwa yayin bude cibiyar ta fasfo

Hukumar Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ta ƙaddamar da cibiyar bayar da ingataccen fasfo na zamani da za ta karaɗe jihohin Edo da Delta.

Hukumar ta ƙaddamar da cibiyar ce a ranar Talatar nan bisa jagorancin Ministan Cikin Gida Rauf Ogbeni Aregbesola da Shugaban NIS, CGI Isah Idris Jere.

Fasfo
CGI Isah Idris yayin da aka tarbe shi a Benin yayin kaddamarwar

Sanarwar da Jami’in hulɗa da jama’a na NIS, ACI Amos Okpu ya fitar, ta bayyana cewa, da yake ƙaddamar da cibiyar, Minista Aregbesola ya ce cibiyar za ta dinga biyan buƙatun masu neman fasfo da suka fito daga yankunan jihohin Edo da Delta.

ADVERTISEMENT

Ministan ya ƙara da cewa, cibiyar za ta kasance ta musamman da za ta kula da ofishoshin fasfo na jihohin guda biyu, saboda ƙara inganta ayyukan samar da fasfo a waɗannan jihohi.

  • Tawagar NIS Ta Kai Ziyarar Aiki A Poland Kan Tsaron Iyakoki

Ya ƙara da cewa bisa ƙaddamar da cibiyar, ofisoshin fasfo na jihohin Edo da Delta za su yi aiki kafaɗa da kafaɗa da sauran wurare da ke yankin kudu maso gabas da kudu maso yamma wajen samun nasarar bunƙasa ɓangaran fasfo na zamani.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Fasfo
CGI Isah Idris Jere (na farko a dama) da sauran manyan baki a fadar Oba na Benin

Minstan ya ce inganta fasfo na zamani wata dama ce da masu buƙatar za su zaɓi nau’in fasfo da suke muradi, kamar mai feji 32 da ke aiki na tsawon shekaru biyar da mai feji 64 da ke aiki na tsawon shekaru biyar da kuma mai feji 64 da ke aiki na tsawon shekaru 10.

Ya ce inganta harkokin fasfo zuwa na zamani hanya ce ta ƙara bunƙasa fasaha, musamman inganta sha’anin taro ta yadda kundayen hukumar da ke ɗauke da bayanai za su yi wahalar kwaikwayo da buga na jabu.

A cewarsa, an samar da wannan cibiya ce domin sauƙaƙa wa masu neman tare da kauce wa wahalar da su zuwa wuri main isa a duk lokacin da suka buƙaci samun fasfo, ta yadda za su yi amfani da na’urar zamani wajen gabatar da buƙatarsu ta samun fasfo cikin kwanciyar hanhali a gidajensu ko kuma a ofishinsu.

Fasfo
Minista Aregbesola yayin da yake kaddamar da ofishin fasfon

Ministan ya jaddada cewa gwamnati tana ƙara wasu shirye-shirye wajen tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya suna samun fasfo cikin sauƙi ba tare da wata wahala ba.

A nasa jawabin, Kwanturola Janar na Hukumar NIS, Isah Jere Idris ya bayyana cewa samar da cibiyar ingantaccen fasfo na zamani da ke Benin na ɗaya daga cikin ƙoƙarin sauye-sauyen da yake aiwatarwa a ɓangaren, musamman wajen ƙara faɗaɗa wa masu neman fasfo hanyoyin samu da kuma zaɓi a kan irin wanda suke muradi.

Ya buƙaci masu neman fasfo da su ziyarci shafin hukumar na intanet a passport.immigration.gov.ng a kowani lokaci, domin biyan kuɗaɗe da kuma gabatar da buƙatar neman fasfo tun kafin lokaci ya ƙure, domin kaucewa cunkoso lokacin da suke buƙata.

Ya ƙara da cewa hukumar ba ta amince da biyan tsabar kuɗi ba, inda ya yi kira da masu nema da su tabbatar sun biya kuɗaɗensu ta shafin intanet tun kafin su ziyarci ofisoshin fasfo lokacin da aka tsara musu.

Tun da farko dai, Gwamnan Jihar Edo, Mista Godwin Noheghase Obaseki ya yaba wa hukumar NIS bisa samar da waɗannan sauye-sauye wajen bayar da fasfo. Ya nuna jin daɗinsa wajen zaɓar garin Benin a matsayin cibiya ta wannan aiki, inda ya sha alwashin cewa gwamnatinsa za ta bayar da duk wata gudummuwa da hukumar take buƙata ciki har da tabbacin goyon bayan ƙudurin aikin gina ofishin fasfo a Auchi.

Fasfo
Minista Aregbesola yana jawabi a fadar Oba na Benin

Bugu da ƙari, Sarkin Benin, Mai Martaba Omo no’ Oba n’Edo Uku Akpolokpolo, Oba Ewuare II, Ogidigan ya yaba wa Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari bisa amincewa da kafa cibiyar ingantaccen fasfon na zamani a masarautarsa. Ya ƙara da cewa shugaban ƙasa ya daɗe yana faranta wa mutanen Jihar Edo rai da kuma ‘yan Nijeriya gaba ɗaya.

Ya tabbatar da cewa zai bayar da goyon baya kan wannan aiki tare da miƙa godiyarsa ga Ministan Harkokin Cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola bisa jagorantar manyan jami’an hukumar NIS da kuma sauran ma’aikatu da suka zo yankinsa.

  • https://passport.immigration.gov.ng/

A cikin waɗanda suka halarci ƙaddamar da katafariyar cibiyar ta fasfo har da Hon. Justice PA Akhikhero wanda ya wakilci Alƙalin-alƙalai na jihar, da shugaban ma’aikatan gwamna da muƙaddashin shugaban jami’ar Ambrose Alli, Farfesa Osarheme Osadolor, da shugabannin rundunar sojojin Nijeriya da sauran jami’an tsaro.

 

 

Fasfo
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Next Post
Al’umar Mai’adua Na Bukatar Gyaran Masallacin Juma’arsu Da Ya Shafe Shekaru Ba Gyara

Al'umar Mai'adua Na Bukatar Gyaran Masallacin Juma'arsu Da Ya Shafe Shekaru Ba Gyara

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.