• English
  • Business News
Tuesday, August 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Murza Gashin Baki, Ta Kori Jami’ai 8, Ta Ladabtar Da Wasu Da Dama

by Sulaiman
3 years ago
in Manyan Labarai
0
NIS Ta Murza Gashin Baki, Ta Kori Jami’ai 8, Ta Ladabtar Da Wasu Da Dama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanturola Janar na Hukumar Shige da Fice ta kasa NIS, CGI Isah Jere Idris MFR ya sanar da korar wasu jami’an hukumar su takwas (8) daga bakin aiki tare da hukunta wasu jami’an 18 da aka samu da aikata laifuka daban-daban da ya saba wa dokar hukumar don ladabtarwa.

Sanarwar ta biyo bayan amincewar Hukumar Gudanarwar Rundunonin da ke karkashin Ma’aikatar Cikin Gida (CDCFIB) wadda a njna cewa munanan ayyukan jami’an sun kasance abin da ma’aikatar ba za ta amince a ce jami’anta ne ke aikata irin wannan halayya ba.

In za a iya tunawa, jami’ai 35 ne ake tuhumarsu a wannan shekara, wadanda aka gabatar a gaban babban kwamitin ladabtarwa (SDC) da kuma na tabbatar da bin tsarin aiki (ORT) don tabbatar da tuhume-tuhume daban-daban na laifuffukan da suka shafi ladabtarwa wanda ake zarginsu da aikatawa, wadanda suka hada da cin zarafi abokan huldarsu, ayyukan Allah wadai, rashin gaskiya, barin wurin aiki ba tare da izinin hukumar ba (AWOL) da sauransu.

Bayan kammala binciken da kwamitocin suka yi, SDC da ORT, an kori jami’ai takwas da suka hada da Babban Sufiritanda na Shige da Fice (CSI), mataimakan Sufiritantanda na Shige da Fice (DSI) biyu, mataimakan Sufiritande na Shige da Fice II (ASI2) da kuma wasu Uku masu kananan mukami.

Bugu da kari, an umurci wani Babban Sufiritanda na Shige da Fice da ya yi takardar ritayar dole yayin da wasu jami’ai tara (9) aka rage musu mukami. Sun hada da Mataimakin Sufiritanda na Shige da Fice II (ASI2) wanda aka maida zuwa matsayin Sufeto na Shige da Fice; da Sufeto biyu da aka maida zuwa mukamin Mataimakin Sufeto; da wasu masu kananan mukamai su shida (6) da aka kwace mukamin da suke kai.

Labarai Masu Nasaba

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

Sannan kuma, akwai wasu Jami’ai tara (9) da aka raba wa takardar gargadi, sun hada da Mataimakin Sufiritanda na Shige da Fice II (ASI2) da Kananan Ma’aikata takwas (8), sannan kwamitocin sun wanke wasu jami’ai shida (6) daga dukkan zarge-zargen da ake yi musu.

Bugu da kari, Kwanturola Janar din ya amince da sauya wa jami’ai 100 da aka tura filin jirgin sama na Legas wurin aiki nan take yayin da ya ba da umurnin tuhumar wasu don tabbatar da zargin da ake musu kan badakala a filin jirgin da aka ba da rahoto kwanan nan kana a san matakin da za a dauka akan su.

Kwanturolan Janar, na amfani da wannan damar don tabbatar wa ‘yan kasa da cewa, Hukumar NIS ba za ta lamunta duk wani hali ko nau’i na halin rashin gaskiya ba ga duk Jami’anta, don haka, yana kira ga jama’a da su ci gaba da bada rahoton duk wani nau’in hali na cin zarafi ko rashin gaskiya a bakin aiki da aka ga jami’in hukumar na aikatawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba A Samu Asarar Rai Ko Daya A Gobarar Da Ta Barke A Shalkwatar NYSC Ba – Hukuma

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Biyu A Harin Nakiya A Kaduna

Related

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

2 hours ago
An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami
Manyan Labarai

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

4 hours ago
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

5 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Batun Rashin Lafiyar Tinubu

9 hours ago
Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi
Manyan Labarai

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

17 hours ago
Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna
Manyan Labarai

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

18 hours ago
Next Post
An Kashe ‘Yan Bindiga A Kasuwa A Zamafara

'Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Biyu A Harin Nakiya A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Sun Yi Bikin Murnar Karɓar Kyautar N23m Daga Bankin STANBIC IBTC

‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Sun Yi Bikin Murnar Karɓar Kyautar N23m Daga Bankin STANBIC IBTC

August 12, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

August 12, 2025
An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

August 12, 2025
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

August 12, 2025
’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

August 12, 2025
Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

August 12, 2025
Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati

Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati

August 12, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Batun Rashin Lafiyar Tinubu

August 12, 2025
Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

August 11, 2025
Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

August 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.