• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Murza Gashin Baki, Ta Kori Jami’ai 8, Ta Ladabtar Da Wasu Da Dama

by Sulaiman
3 years ago
in Manyan Labarai
0
NIS Ta Murza Gashin Baki, Ta Kori Jami’ai 8, Ta Ladabtar Da Wasu Da Dama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanturola Janar na Hukumar Shige da Fice ta kasa NIS, CGI Isah Jere Idris MFR ya sanar da korar wasu jami’an hukumar su takwas (8) daga bakin aiki tare da hukunta wasu jami’an 18 da aka samu da aikata laifuka daban-daban da ya saba wa dokar hukumar don ladabtarwa.

Sanarwar ta biyo bayan amincewar Hukumar Gudanarwar Rundunonin da ke karkashin Ma’aikatar Cikin Gida (CDCFIB) wadda a njna cewa munanan ayyukan jami’an sun kasance abin da ma’aikatar ba za ta amince a ce jami’anta ne ke aikata irin wannan halayya ba.

In za a iya tunawa, jami’ai 35 ne ake tuhumarsu a wannan shekara, wadanda aka gabatar a gaban babban kwamitin ladabtarwa (SDC) da kuma na tabbatar da bin tsarin aiki (ORT) don tabbatar da tuhume-tuhume daban-daban na laifuffukan da suka shafi ladabtarwa wanda ake zarginsu da aikatawa, wadanda suka hada da cin zarafi abokan huldarsu, ayyukan Allah wadai, rashin gaskiya, barin wurin aiki ba tare da izinin hukumar ba (AWOL) da sauransu.

Bayan kammala binciken da kwamitocin suka yi, SDC da ORT, an kori jami’ai takwas da suka hada da Babban Sufiritanda na Shige da Fice (CSI), mataimakan Sufiritantanda na Shige da Fice (DSI) biyu, mataimakan Sufiritande na Shige da Fice II (ASI2) da kuma wasu Uku masu kananan mukami.

Bugu da kari, an umurci wani Babban Sufiritanda na Shige da Fice da ya yi takardar ritayar dole yayin da wasu jami’ai tara (9) aka rage musu mukami. Sun hada da Mataimakin Sufiritanda na Shige da Fice II (ASI2) wanda aka maida zuwa matsayin Sufeto na Shige da Fice; da Sufeto biyu da aka maida zuwa mukamin Mataimakin Sufeto; da wasu masu kananan mukamai su shida (6) da aka kwace mukamin da suke kai.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba

Sannan kuma, akwai wasu Jami’ai tara (9) da aka raba wa takardar gargadi, sun hada da Mataimakin Sufiritanda na Shige da Fice II (ASI2) da Kananan Ma’aikata takwas (8), sannan kwamitocin sun wanke wasu jami’ai shida (6) daga dukkan zarge-zargen da ake yi musu.

Bugu da kari, Kwanturola Janar din ya amince da sauya wa jami’ai 100 da aka tura filin jirgin sama na Legas wurin aiki nan take yayin da ya ba da umurnin tuhumar wasu don tabbatar da zargin da ake musu kan badakala a filin jirgin da aka ba da rahoto kwanan nan kana a san matakin da za a dauka akan su.

Kwanturolan Janar, na amfani da wannan damar don tabbatar wa ‘yan kasa da cewa, Hukumar NIS ba za ta lamunta duk wani hali ko nau’i na halin rashin gaskiya ba ga duk Jami’anta, don haka, yana kira ga jama’a da su ci gaba da bada rahoton duk wani nau’in hali na cin zarafi ko rashin gaskiya a bakin aiki da aka ga jami’in hukumar na aikatawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba A Samu Asarar Rai Ko Daya A Gobarar Da Ta Barke A Shalkwatar NYSC Ba – Hukuma

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Biyu A Harin Nakiya A Kaduna

Related

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

9 hours ago
Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba

14 hours ago
Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya
Manyan Labarai

Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya

19 hours ago
Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu
Manyan Labarai

Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu

1 day ago
Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ
Tsaro

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

1 day ago
Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

1 day ago
Next Post
An Kashe ‘Yan Bindiga A Kasuwa A Zamafara

'Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Biyu A Harin Nakiya A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.