• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Sake Lashe Kambun Gwarzuwar Hukuma Mafi Kwazo

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
NIS Ta Sake Lashe Kambun Gwarzuwar Hukuma Mafi Kwazo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ta sake samun nasarar lashe kambun zama gwarzuwar hukuma mafi ƙwazo a cikin hukumomin gwamnati a bangaren shawo kan korafe-korafe a watan Agustan 2022.

Majalisar da shugaban ƙasa ya kafa a a kan kyatata yanayin hada-hadar kasuwanci (PEBEC) ta sanar da hakan a wani rahoton da ta fitar na suna kokarin hukumomi, Ma’aikatu, rassan gwamnatin na watan Agustan 2022.

Kamar yadda jami’in hulɗa da jama’a na NIS, DCI Amos Okpu, ya bayyana a wata sanarwa da ya fitar yau Lahadi, domin inganta aiki da lamuran da suka shafi samar da kyakkyawan yanayi na hada-hada, PEBEC ta fitar da wani tsari domin gano kokarin ma’aikatu da hukumomin gwamnati ko gazawarsu tare da hanyoyin da suke bi wajen shawo kan matsalolin jama’a masu hulɗa da Ma’aikatunsu.

  • Mutane 9 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata A Wani Hatsarin Mota Da Ya Rutsa Da Su A Abuja

Ya ce, daga cikin hanyoyin aiki da majalisar PEBEC ta sanar akwai shafin intanet na reportgov.ng wanda jama’a za su rika samun damar tuntubar ma’aikatu da hukumomi domin shigar da korafe-korafe ko kokensu ko wata gazawar da suka gani da ta shafi wata hukuma kuma ana tsammanin ma’aikatar da lamarin ya shafa za ta amsa wannan korafin ko koken cikin awanni 72.

“Kan haka ne hukumar PEBEC ta gabatar da tsarin duba kokarin Ma’aikatu a wata-wata domin duba yadda aka yi kokari ko akasinsa don kyautata aiki bisa yadda aka tsara.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

“Kan amsa korafin jama’a cikin hanzari kuma a kan lokaci ne ta ofishin kula da aiki ya sanya hukumar Immigration ta lashe kambun hukuma mafi kwazo a watan Agustan 2022.”

Da ya ke tofa albarkacin bakinsa kan wannan nasarar, Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS), Isah Jere Idris, ya nuna matuƙar jin daɗi da wannan nasara tare da yaba wa ƙoƙarin jami’ansa da suka zage damtse suka yi aiki sosai domin farfaɗo da tsarin aiki a kowane lokaci.

Ya ba da tabbacin cewa zai ci gaba da himma wajen tabbatar da walwalar jami’ai da kyautata yanayin aiki da saka wa jami’an da suka yi ƙoƙari daidai gwargwadon abin da hukumar take da shi a hannu.

Jere ya jawo hankalin al’ummar kasar nan da a kowani lokaci su riƙa sanar da hukumar duk wani abun da suka fuskanta na kalubale ko rashin bin ka’idar aiki daga wani jami’in hukumar domin daukar matakan da suka dace.

Idan za ku iya tunawa dai wannan lambar yabon da hukumar kula da shige da fice ta samu shi ne karo na hudu a wannan shekarar daga wajen PEBEC domin ta samu irinsa a watan Afrilu, Mayu da Yuni sai kuma Agusta.

  • https://leadership.ng/nis-redeploys-69-senior-officers/nigeria-immigration-service/

Ita dai majalisar da shugaban ƙasa ya kafa a kan kyautata yanayin hada-hada (PEBEC) an kaddamar da ita ce domin inganta harkokin kasuwanci a Nijeriya, zuwa yanzu mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo yake jagorantar ta.

Wannan lambar yabo da NIS ta lashe ya ƙara fayyace namijin ƙoƙarin da hukumar bisa jagorancin shugabanta, Isah Jere Idris ke yi na kyautata mu’amala da abokan hulɗarta da kuma ƙwazon aiki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ra’ayoyinku Kan Sabon Yajin Aiki Da ASUU Ta Tsunduma

Next Post

Ko Budurwa Na Da Hannu A Rashin Cika Alkawarin Saurayinta?

Related

Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

2 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

2 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

3 hours ago
Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

4 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

8 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

17 hours ago
Next Post
Ko Budurwa Na Da Hannu A Rashin Cika Alkawarin Saurayinta?

Ko Budurwa Na Da Hannu A Rashin Cika Alkawarin Saurayinta?

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

September 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

September 14, 2025
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.