• English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Sake Lashe Kambun Gwarzuwar Hukuma Mafi Kwazo

by Khalid Idris Doya
3 years ago
NIS

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ta sake samun nasarar lashe kambun zama gwarzuwar hukuma mafi ƙwazo a cikin hukumomin gwamnati a bangaren shawo kan korafe-korafe a watan Agustan 2022.

Majalisar da shugaban ƙasa ya kafa a a kan kyatata yanayin hada-hadar kasuwanci (PEBEC) ta sanar da hakan a wani rahoton da ta fitar na suna kokarin hukumomi, Ma’aikatu, rassan gwamnatin na watan Agustan 2022.

Kamar yadda jami’in hulɗa da jama’a na NIS, DCI Amos Okpu, ya bayyana a wata sanarwa da ya fitar yau Lahadi, domin inganta aiki da lamuran da suka shafi samar da kyakkyawan yanayi na hada-hada, PEBEC ta fitar da wani tsari domin gano kokarin ma’aikatu da hukumomin gwamnati ko gazawarsu tare da hanyoyin da suke bi wajen shawo kan matsalolin jama’a masu hulɗa da Ma’aikatunsu.

  • Mutane 9 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata A Wani Hatsarin Mota Da Ya Rutsa Da Su A Abuja

Ya ce, daga cikin hanyoyin aiki da majalisar PEBEC ta sanar akwai shafin intanet na reportgov.ng wanda jama’a za su rika samun damar tuntubar ma’aikatu da hukumomi domin shigar da korafe-korafe ko kokensu ko wata gazawar da suka gani da ta shafi wata hukuma kuma ana tsammanin ma’aikatar da lamarin ya shafa za ta amsa wannan korafin ko koken cikin awanni 72.

“Kan haka ne hukumar PEBEC ta gabatar da tsarin duba kokarin Ma’aikatu a wata-wata domin duba yadda aka yi kokari ko akasinsa don kyautata aiki bisa yadda aka tsara.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

“Kan amsa korafin jama’a cikin hanzari kuma a kan lokaci ne ta ofishin kula da aiki ya sanya hukumar Immigration ta lashe kambun hukuma mafi kwazo a watan Agustan 2022.”

Da ya ke tofa albarkacin bakinsa kan wannan nasarar, Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS), Isah Jere Idris, ya nuna matuƙar jin daɗi da wannan nasara tare da yaba wa ƙoƙarin jami’ansa da suka zage damtse suka yi aiki sosai domin farfaɗo da tsarin aiki a kowane lokaci.

Ya ba da tabbacin cewa zai ci gaba da himma wajen tabbatar da walwalar jami’ai da kyautata yanayin aiki da saka wa jami’an da suka yi ƙoƙari daidai gwargwadon abin da hukumar take da shi a hannu.

Jere ya jawo hankalin al’ummar kasar nan da a kowani lokaci su riƙa sanar da hukumar duk wani abun da suka fuskanta na kalubale ko rashin bin ka’idar aiki daga wani jami’in hukumar domin daukar matakan da suka dace.

Idan za ku iya tunawa dai wannan lambar yabon da hukumar kula da shige da fice ta samu shi ne karo na hudu a wannan shekarar daga wajen PEBEC domin ta samu irinsa a watan Afrilu, Mayu da Yuni sai kuma Agusta.

  • https://leadership.ng/nis-redeploys-69-senior-officers/nigeria-immigration-service/

Ita dai majalisar da shugaban ƙasa ya kafa a kan kyautata yanayin hada-hada (PEBEC) an kaddamar da ita ce domin inganta harkokin kasuwanci a Nijeriya, zuwa yanzu mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo yake jagorantar ta.

Wannan lambar yabo da NIS ta lashe ya ƙara fayyace namijin ƙoƙarin da hukumar bisa jagorancin shugabanta, Isah Jere Idris ke yi na kyautata mu’amala da abokan hulɗarta da kuma ƙwazon aiki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025
Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

November 10, 2025
Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump
Manyan Labarai

Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

November 10, 2025
Next Post
Ko Budurwa Na Da Hannu A Rashin Cika Alkawarin Saurayinta?

Ko Budurwa Na Da Hannu A Rashin Cika Alkawarin Saurayinta?

LABARAI MASU NASABA

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

November 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025
Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

November 10, 2025
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

November 10, 2025
Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

November 10, 2025
Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

November 10, 2025
Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

November 10, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Zai Ziyarci Kasashen Guinea Da Saliyo

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Zai Ziyarci Kasashen Guinea Da Saliyo

November 10, 2025
FCT Ta Saka Ranar 1 Disamba Don Kammala Biyan Kudin Hajjin 2026 N7.7m

FCT Ta Saka Ranar 1 Disamba Don Kammala Biyan Kudin Hajjin 2026 N7.7m

November 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.