• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Sake Lashe Kambun Gwarzuwar Hukuma Mafi Kwazo

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
NIS Ta Sake Lashe Kambun Gwarzuwar Hukuma Mafi Kwazo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ta sake samun nasarar lashe kambun zama gwarzuwar hukuma mafi ƙwazo a cikin hukumomin gwamnati a bangaren shawo kan korafe-korafe a watan Agustan 2022.

Majalisar da shugaban ƙasa ya kafa a a kan kyatata yanayin hada-hadar kasuwanci (PEBEC) ta sanar da hakan a wani rahoton da ta fitar na suna kokarin hukumomi, Ma’aikatu, rassan gwamnatin na watan Agustan 2022.

Kamar yadda jami’in hulɗa da jama’a na NIS, DCI Amos Okpu, ya bayyana a wata sanarwa da ya fitar yau Lahadi, domin inganta aiki da lamuran da suka shafi samar da kyakkyawan yanayi na hada-hada, PEBEC ta fitar da wani tsari domin gano kokarin ma’aikatu da hukumomin gwamnati ko gazawarsu tare da hanyoyin da suke bi wajen shawo kan matsalolin jama’a masu hulɗa da Ma’aikatunsu.

  • Mutane 9 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata A Wani Hatsarin Mota Da Ya Rutsa Da Su A Abuja

Ya ce, daga cikin hanyoyin aiki da majalisar PEBEC ta sanar akwai shafin intanet na reportgov.ng wanda jama’a za su rika samun damar tuntubar ma’aikatu da hukumomi domin shigar da korafe-korafe ko kokensu ko wata gazawar da suka gani da ta shafi wata hukuma kuma ana tsammanin ma’aikatar da lamarin ya shafa za ta amsa wannan korafin ko koken cikin awanni 72.

“Kan haka ne hukumar PEBEC ta gabatar da tsarin duba kokarin Ma’aikatu a wata-wata domin duba yadda aka yi kokari ko akasinsa don kyautata aiki bisa yadda aka tsara.

Labarai Masu Nasaba

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

“Kan amsa korafin jama’a cikin hanzari kuma a kan lokaci ne ta ofishin kula da aiki ya sanya hukumar Immigration ta lashe kambun hukuma mafi kwazo a watan Agustan 2022.”

Da ya ke tofa albarkacin bakinsa kan wannan nasarar, Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS), Isah Jere Idris, ya nuna matuƙar jin daɗi da wannan nasara tare da yaba wa ƙoƙarin jami’ansa da suka zage damtse suka yi aiki sosai domin farfaɗo da tsarin aiki a kowane lokaci.

Ya ba da tabbacin cewa zai ci gaba da himma wajen tabbatar da walwalar jami’ai da kyautata yanayin aiki da saka wa jami’an da suka yi ƙoƙari daidai gwargwadon abin da hukumar take da shi a hannu.

Jere ya jawo hankalin al’ummar kasar nan da a kowani lokaci su riƙa sanar da hukumar duk wani abun da suka fuskanta na kalubale ko rashin bin ka’idar aiki daga wani jami’in hukumar domin daukar matakan da suka dace.

Idan za ku iya tunawa dai wannan lambar yabon da hukumar kula da shige da fice ta samu shi ne karo na hudu a wannan shekarar daga wajen PEBEC domin ta samu irinsa a watan Afrilu, Mayu da Yuni sai kuma Agusta.

  • https://leadership.ng/nis-redeploys-69-senior-officers/nigeria-immigration-service/

Ita dai majalisar da shugaban ƙasa ya kafa a kan kyautata yanayin hada-hada (PEBEC) an kaddamar da ita ce domin inganta harkokin kasuwanci a Nijeriya, zuwa yanzu mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo yake jagorantar ta.

Wannan lambar yabo da NIS ta lashe ya ƙara fayyace namijin ƙoƙarin da hukumar bisa jagorancin shugabanta, Isah Jere Idris ke yi na kyautata mu’amala da abokan hulɗarta da kuma ƙwazon aiki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ra’ayoyinku Kan Sabon Yajin Aiki Da ASUU Ta Tsunduma

Next Post

Ko Budurwa Na Da Hannu A Rashin Cika Alkawarin Saurayinta?

Related

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

31 minutes ago
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

2 hours ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

3 hours ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

4 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

5 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

6 hours ago
Next Post
Ko Budurwa Na Da Hannu A Rashin Cika Alkawarin Saurayinta?

Ko Budurwa Na Da Hannu A Rashin Cika Alkawarin Saurayinta?

LABARAI MASU NASABA

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.