• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Sake Lashe Kambun Gwarzuwar Hukuma Mafi Kwazo

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
NIS Ta Sake Lashe Kambun Gwarzuwar Hukuma Mafi Kwazo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ta sake samun nasarar lashe kambun zama gwarzuwar hukuma mafi ƙwazo a cikin hukumomin gwamnati a bangaren shawo kan korafe-korafe a watan Agustan 2022.

Majalisar da shugaban ƙasa ya kafa a a kan kyatata yanayin hada-hadar kasuwanci (PEBEC) ta sanar da hakan a wani rahoton da ta fitar na suna kokarin hukumomi, Ma’aikatu, rassan gwamnatin na watan Agustan 2022.

Kamar yadda jami’in hulɗa da jama’a na NIS, DCI Amos Okpu, ya bayyana a wata sanarwa da ya fitar yau Lahadi, domin inganta aiki da lamuran da suka shafi samar da kyakkyawan yanayi na hada-hada, PEBEC ta fitar da wani tsari domin gano kokarin ma’aikatu da hukumomin gwamnati ko gazawarsu tare da hanyoyin da suke bi wajen shawo kan matsalolin jama’a masu hulɗa da Ma’aikatunsu.

  • Mutane 9 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata A Wani Hatsarin Mota Da Ya Rutsa Da Su A Abuja

Ya ce, daga cikin hanyoyin aiki da majalisar PEBEC ta sanar akwai shafin intanet na reportgov.ng wanda jama’a za su rika samun damar tuntubar ma’aikatu da hukumomi domin shigar da korafe-korafe ko kokensu ko wata gazawar da suka gani da ta shafi wata hukuma kuma ana tsammanin ma’aikatar da lamarin ya shafa za ta amsa wannan korafin ko koken cikin awanni 72.

“Kan haka ne hukumar PEBEC ta gabatar da tsarin duba kokarin Ma’aikatu a wata-wata domin duba yadda aka yi kokari ko akasinsa don kyautata aiki bisa yadda aka tsara.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo

“Kan amsa korafin jama’a cikin hanzari kuma a kan lokaci ne ta ofishin kula da aiki ya sanya hukumar Immigration ta lashe kambun hukuma mafi kwazo a watan Agustan 2022.”

Da ya ke tofa albarkacin bakinsa kan wannan nasarar, Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS), Isah Jere Idris, ya nuna matuƙar jin daɗi da wannan nasara tare da yaba wa ƙoƙarin jami’ansa da suka zage damtse suka yi aiki sosai domin farfaɗo da tsarin aiki a kowane lokaci.

Ya ba da tabbacin cewa zai ci gaba da himma wajen tabbatar da walwalar jami’ai da kyautata yanayin aiki da saka wa jami’an da suka yi ƙoƙari daidai gwargwadon abin da hukumar take da shi a hannu.

Jere ya jawo hankalin al’ummar kasar nan da a kowani lokaci su riƙa sanar da hukumar duk wani abun da suka fuskanta na kalubale ko rashin bin ka’idar aiki daga wani jami’in hukumar domin daukar matakan da suka dace.

Idan za ku iya tunawa dai wannan lambar yabon da hukumar kula da shige da fice ta samu shi ne karo na hudu a wannan shekarar daga wajen PEBEC domin ta samu irinsa a watan Afrilu, Mayu da Yuni sai kuma Agusta.

  • https://leadership.ng/nis-redeploys-69-senior-officers/nigeria-immigration-service/

Ita dai majalisar da shugaban ƙasa ya kafa a kan kyautata yanayin hada-hada (PEBEC) an kaddamar da ita ce domin inganta harkokin kasuwanci a Nijeriya, zuwa yanzu mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo yake jagorantar ta.

Wannan lambar yabo da NIS ta lashe ya ƙara fayyace namijin ƙoƙarin da hukumar bisa jagorancin shugabanta, Isah Jere Idris ke yi na kyautata mu’amala da abokan hulɗarta da kuma ƙwazon aiki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ra’ayoyinku Kan Sabon Yajin Aiki Da ASUU Ta Tsunduma

Next Post

Ko Budurwa Na Da Hannu A Rashin Cika Alkawarin Saurayinta?

Related

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

59 minutes ago
Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo
Manyan Labarai

Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo

3 hours ago
Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC
Manyan Labarai

Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC

4 hours ago
Kotu Ta Ɗage Yanke Hukunci Kan Neman Izinin Jinyar Yahaya Bello
Labarai

Kotu Ta Ɗage Yanke Hukunci Kan Neman Izinin Jinyar Yahaya Bello

6 hours ago
ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni
Manyan Labarai

ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni

10 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Labarai

‘Yansanda Sun Kuɓutar Da ‘Yan Ghana 19 Da Aka Yaudare Su Zuwa Nijeriya

13 hours ago
Next Post
Ko Budurwa Na Da Hannu A Rashin Cika Alkawarin Saurayinta?

Ko Budurwa Na Da Hannu A Rashin Cika Alkawarin Saurayinta?

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

July 8, 2025
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

July 8, 2025
Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

July 8, 2025
Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo

Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo

July 8, 2025
Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka

Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka

July 8, 2025
Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC

Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC

July 8, 2025
An Bude Taron Layin Dogo Mai Saurin Gudu Na Duniya Karo Na 12 A Beijing

An Bude Taron Layin Dogo Mai Saurin Gudu Na Duniya Karo Na 12 A Beijing

July 8, 2025
Ahmed Musa Ya Ƙaryata Kyautar Motoci Ga Ƴan Wasa Da Ma’aikatan Kano Pillars

Ahmed Musa Ya Ƙaryata Kyautar Motoci Ga Ƴan Wasa Da Ma’aikatan Kano Pillars

July 8, 2025
Sin Za Ta Yi Aiki Da MDD Don Samar Da Jagorancin Duniya Mai Cike Da Adalci Da Daidaito

Sin Za Ta Yi Aiki Da MDD Don Samar Da Jagorancin Duniya Mai Cike Da Adalci Da Daidaito

July 8, 2025
Xi: Ana Kokarin Rubuta Sabon Babi Na Zamanantar Da Sin A Lardin Shanxi

Xi: Ana Kokarin Rubuta Sabon Babi Na Zamanantar Da Sin A Lardin Shanxi

July 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.