• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Samar Da Fasfo Kimanin Miliyan 2 A Shekarar 2022 —Gwamnatin Tarayya

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
NIS Ta Samar Da Fasfo Kimanin Miliyan 2 A Shekarar 2022 —Gwamnatin Tarayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta ce, akalla Fasfo Miliyan 1.9 hukumar kula da shige da fice ta kasa (NIS) ta samar a shekarar 2022 da ta gabata, da ke nuna an samu ci gaba da kusan kashi 80 cikin 100 kan wanda aka samar a 2021.

Ministan kula da harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola, ne ya shaida hakan a ranar Litinin yayin kaddamar da ofishin karba da shigar da bayanan Fasfo da ke Alimosho a Jihar Legas.

  • Shugaba Buhari Ya Karrama CGI Isah Jere Da Lambar Yabo Ta Ƙasa Bisa Mutunta Ɗan’adam A Shugabancinsa
  • Shugaban NIS Isah Jere Ya Sanar Da Ƙarin Girma Ga Jami’ai 4,526

An samar da ofishin ne a wani mataki na samar da dabarun tabbatar da aikin Fasfo don tafiya cikin sauki da hanzari ga ‘Yan Nijeriya.

Ministan ya kuma ce, hakan zai rage wahalhalun da ake sha wajen aikin Fasfo a Legas.

“Mun dukufa wajen fadada ayyukanmu na samar da Fasfo domin cike gibin karancin da ake yawan samu a manyan birane musamman irin su Legas. Wannan dalilin ne ya sanya aka samar da ofishin Fasfo a Alimosho da zai rage nauyi ga wasu ofisoshin Fasfo uku da suke Legas.”

Labarai Masu Nasaba

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

Aregbesola ya kara da cewa, NIS na aiki tukuru wajen kara himma da azama a bangaren samar da Fasfo domin biyan bukatun masu nema da shawo kan matsalolin da ake fuskanta.

“Bukatun Fasfo na karuwa duk shekara sakamakon yadda ‘Yan Nijeriya da dama ke bukatar fita kasashen waje da kuma wadanda suke son mallakar Fasfo din a matsayin shaida.

“Amma mun kara yawan wuraren yin aikin. A shekarar da ta gabata mun kuma samar da Fasfo Miliyan 1.9, sabanin miliyan 1 da muka samar a 2021.”

Ministan ya yi karin hasken cewa ofishin da aka bude a Alimosho zai rika amsar zallar bukatun masu neman fasfo, amma ba wai waje ne da za a rika wallafa fasfon ba.

Duk da hakan ministan ya ce akwai bukatar kara samar da wasu ofisoshin yin Fasfo a kalla guda 15 a Legas sakamakon cewa jihar ita ce take da kusan rabin dukkan fasfon da ake gabatar da bukatar nema a Nijeriya.

Aregbesola ya kuma jadadda cewa babu makawa a shigar da kamfanoni masu zaman kansu wajen samar da wadannan ofisoshin na karba da shigar da bayanan fasfo a Legas, saboda kalubalen kudade da gwamnati ke fuskanta, domin hakan zai rage tsawon lokacin da ake kwashe wajen jiran fasfo.

“Amma saboda kalubalen kudade, gwamnati bata iya samar da wadannan ofisoshi, don haka za mu bukaci abokan hulda masu zaman kansu da za su samar da ofishin, abin da kawai za su yi shi ne samar da ofisoshin amma jami’an shige da fice ne za su rika kula da su tare da gudanar da su.

“Tabbas muna bukatar karin wannan a Legas. Hakan ya faru ne saboda rabin duk takardun fasfo ana yin su ne a Legas.”
Aregbesola ya kuma yi kira ga masu bukatar fasfo da su rika yi da kansu a ofisoshin NIS ba tare da mu’amala da marasa gaskiya ba.

Tun da farko dai, Aregbesola ya kaddamar da hedikwatar hukumar shige da fice ta Nijeriya (NIS) reshen Jihar Legas da ke Ikoyi.

Ya bayyana cewa kaddamar da ofishin na daya daga cikin ci gaban da ma’aikatar harkokin cikin gida ta samar a karkashin gwamnatin shugaban kasa, Muhammadu Buhari.

“Tun da aka nada ni a matsayin minista, mun kaddamar da sabbin hedikwatocin jihohi 17 a fadin kasar nan na hukumar NIS, inda ta Legas ita ce ta 18.

Kokarin da gwamnatin Shugaba, Muhammadu Buhari, take yi na ganin an kara tabbatar da tsaron iyakokinmu ya sa aka samar da sabbin ofisoshi na kula da sintiri da inganta Tsarin Kula da Iyakoki na zamani bisa doka”. In ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JereNISShige Da Fice
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Shawo Kan Amfani Da Karfin Tuwo Da Jami’an Tsaro Ke Yi Kan Fararen Hula

Next Post

Shugaban NIS Ya Sake Gargadin Marasa Gaskiya A Kan Harkokin Fasfo

Related

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari
Rahotonni

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

2 hours ago
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

11 hours ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

12 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

12 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

13 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

15 hours ago
Next Post
Ba Za Mu Yi Kasa A Guiwa Wajen Tabbatar Da Ingantaccen Aiki Ga Al’umma Ba – Shugaban NIS

Shugaban NIS Ya Sake Gargadin Marasa Gaskiya A Kan Harkokin Fasfo

LABARAI MASU NASABA

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.