• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Yi Wa Manyan Jami’ai 98 Ado Da Sabbin Muƙamansu

by yahuzajere
3 years ago
in Labarai
0
NIS Ta Yi Wa Manyan Jami’ai 98 Ado Da Sabbin Muƙamansu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS), CGI Isah Idris Jere ya yi wa manyan jami’ai 94 da suka samu ƙarin girma ado da sababbin muƙamansu a shalkwatar hukumar da ke Abuja, yayin da ragowar huxun aka yi musu a Ma’aikatar Cikin Gida.

Wannan ya biyo bayan amincewa da ƙarin girma ga manyan jami’an ne da Hukumar Gudanarwar Rundunonin Ma’aikatar Cikin Gida (CDCFIB) ta yi tare da fitar da sunayen waxanda suka samu a shekarar 2022 a can kwanan baya.

  • Atiku Zai Yi Wa Tinubu Kwab Ɗaya, Don Ba Tsaransa Ba Ne, In Ji PDP

Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulxa da jama’a na NIS, ACI Amos Okpu ta bayyana cewa jimillar sabbin waxanda aka ƙara wa girma zuwa muƙamin ƙananan mataimakan Kwanturola Janar 24 da Kwanturololi 70 aka yi musu ado da sabbin muƙaman a wani ƙwarya-ƙwaryan biki da ya samu halartar takwarorin NIS da ke ƙarƙashin Ma’aikatar Cikin Gida da sauran manyan jagororin Hukumar CDCFIB.

NIS

Da yake jawabi a wurin, Shugaban NIS, Isah Jere ya bayyana cewa ƙarin girman da jami’an suka samu ya nuna ɓaro-ɓaro a fili irin yadda hukumar ta mayar da hankali ga inganta walwalar jami’anta. Ya nunar da cewa wannan yana daga cikin manyan ƙudurori uku da yake son cimmawa tun daga lokacin da ya karɓi ragamar shugabancin hukumar da suka haxa da inganta tsaron iyakokin ƙasa, gyarar fuska ga ayyukan fasfo sai kuma kyautata jin daxi da walwalar jami’ai.

Labarai Masu Nasaba

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

NIS

Ya hori sabbin jami’an da suka samu ƙarin girman su ƙara duƙufa sosai ga aiki da kula da ayyukan na ƙasa da su domin tabbatar da ayyuka sun inganta a hukumar a samu xorewar ci gaban da ake samu. Ya ƙara da cewa, hukumar ba za ta lamunci raggonci ba daga gare su musamman ta ɓangaren da ake ganin ana iya cimma nasara xari bisa xari.

Tun da farko dai, Sakatariyar Hukumar Gudanarwa ta CDCFIB, Hajiya Aisha Rufa’i ta taya sabbin masu muƙaman murna bisa ci gaban da suka samu ta la’akari da cancanta, tana mai jaddada cewa hukumar ta yi nazari sosai a kan halaye da xabi’unsu, da ƙwazonsu na aiki da iya zance da sauran dabarun da ake buƙatar gani kafin a yi wa manyan jami’ai ƙarin girma.

NIS

Wakazalika, shi ma Kwamishinan Hukumar Gudanarwar mai kula da xaukar aiki da ƙarin girma, Manjo Janar Emmanuel Bassey mai ritaya, ya yi kira ga jami’an da aka ƙara wa girman su jagoranci sauran ma’aikata da ke ƙarƙashinsu cikin dattaku da kamun kai sannan a koyaushe ya zama suna cikin shirin aiki bisa ƙwarewa da xa’a a matsayinsu na manyan jami’ai.

Daga cikin manyan jami’an da aka saka musu sabbin muƙaman nasu na ƙananan mataimakan Kwanturola Janar akwai ACG Kemi Nandap, babbar jami’ar da ke kula da shige da fice a Filin Jiragen Sama na Murtala Muhammad da ke Legas, da babban jami’in harkokin ofishin CGI da aka sauya kwanan nan, ACG Ahmad Bauchi Aliyu da kuma Kwanturola Mustapha Ahmad, mataimaki na musamman ga CGI a fannin gudanar da ayyuka.

A halin da ake ciki kuma, Ministan Cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola a ranar Talata ya sanya wa sababbin jami’ai da aka naxa a matsayin manyan mataimakan Kwanturola Janar muƙamansu, a babban xakin taro na ma’aikatar. Waxanda aka yi wa ado da muƙaman sun haxa da DCG Oluremi Talabi, DCG Josephine Kwazu, DCG Modupe Anyalechi da kuma DCG Muhammad Aminu Muhammad.

NIS

Ministan ya taya su murna a kan sabbin muƙaman nasu kana ya nemi su yi amfani da basirarsu da ƙwarewar aiki wajen yaƙi da rashin tsaro a ƙasar nan.

Daga cikin manyan mutanen da suka halarci bikin maƙala sabbin muƙaman na NIS akwai Kwamishinan Tarayya na Hukumar Gudanarwa ta CDCFIB, ACG Ado Jaffaru (mai ritaya), da Sanata Uba Sani, da Sakataren Gwamnatin Jihar Kaduna, Malam Bala Abbas Lawal, da wakilan shugabannin rundunonin da ke ƙarƙashin ma’aikatar cikin gida da sauransu.

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Atiku Zai Yi Wa Tinubu Kwab Ɗaya, Don Ba Tsaransa Ba Ne, In Ji PDP

Next Post

Gwamnatin Tarayya Ta Samu Naira Biliyan 19.2 Daga Fannin Zinare A Kwatar Shekara

Related

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi
Manyan Labarai

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

32 minutes ago
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita
Labarai

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

11 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

13 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

15 hours ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

15 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

18 hours ago
Next Post
NIS

Gwamnatin Tarayya Ta Samu Naira Biliyan 19.2 Daga Fannin Zinare A Kwatar Shekara

LABARAI MASU NASABA

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.