• English
  • Business News
Sunday, October 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Yi Wa Manyan Jami’ai 98 Ado Da Sabbin Muƙamansu

by yahuzajere
3 years ago
NIS

Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS), CGI Isah Idris Jere ya yi wa manyan jami’ai 94 da suka samu ƙarin girma ado da sababbin muƙamansu a shalkwatar hukumar da ke Abuja, yayin da ragowar huxun aka yi musu a Ma’aikatar Cikin Gida.

Wannan ya biyo bayan amincewa da ƙarin girma ga manyan jami’an ne da Hukumar Gudanarwar Rundunonin Ma’aikatar Cikin Gida (CDCFIB) ta yi tare da fitar da sunayen waxanda suka samu a shekarar 2022 a can kwanan baya.

  • Atiku Zai Yi Wa Tinubu Kwab Ɗaya, Don Ba Tsaransa Ba Ne, In Ji PDP

Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulxa da jama’a na NIS, ACI Amos Okpu ta bayyana cewa jimillar sabbin waxanda aka ƙara wa girma zuwa muƙamin ƙananan mataimakan Kwanturola Janar 24 da Kwanturololi 70 aka yi musu ado da sabbin muƙaman a wani ƙwarya-ƙwaryan biki da ya samu halartar takwarorin NIS da ke ƙarƙashin Ma’aikatar Cikin Gida da sauran manyan jagororin Hukumar CDCFIB.

NIS

Da yake jawabi a wurin, Shugaban NIS, Isah Jere ya bayyana cewa ƙarin girman da jami’an suka samu ya nuna ɓaro-ɓaro a fili irin yadda hukumar ta mayar da hankali ga inganta walwalar jami’anta. Ya nunar da cewa wannan yana daga cikin manyan ƙudurori uku da yake son cimmawa tun daga lokacin da ya karɓi ragamar shugabancin hukumar da suka haxa da inganta tsaron iyakokin ƙasa, gyarar fuska ga ayyukan fasfo sai kuma kyautata jin daxi da walwalar jami’ai.

LABARAI MASU NASABA

Trump Da Al-Sisi Za Su Jagoranci Taron Zaman Lafiya Dawwamammiya Ta Gaza A Masar

Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor

NIS

Ya hori sabbin jami’an da suka samu ƙarin girman su ƙara duƙufa sosai ga aiki da kula da ayyukan na ƙasa da su domin tabbatar da ayyuka sun inganta a hukumar a samu xorewar ci gaban da ake samu. Ya ƙara da cewa, hukumar ba za ta lamunci raggonci ba daga gare su musamman ta ɓangaren da ake ganin ana iya cimma nasara xari bisa xari.

Tun da farko dai, Sakatariyar Hukumar Gudanarwa ta CDCFIB, Hajiya Aisha Rufa’i ta taya sabbin masu muƙaman murna bisa ci gaban da suka samu ta la’akari da cancanta, tana mai jaddada cewa hukumar ta yi nazari sosai a kan halaye da xabi’unsu, da ƙwazonsu na aiki da iya zance da sauran dabarun da ake buƙatar gani kafin a yi wa manyan jami’ai ƙarin girma.

NIS

Wakazalika, shi ma Kwamishinan Hukumar Gudanarwar mai kula da xaukar aiki da ƙarin girma, Manjo Janar Emmanuel Bassey mai ritaya, ya yi kira ga jami’an da aka ƙara wa girman su jagoranci sauran ma’aikata da ke ƙarƙashinsu cikin dattaku da kamun kai sannan a koyaushe ya zama suna cikin shirin aiki bisa ƙwarewa da xa’a a matsayinsu na manyan jami’ai.

Daga cikin manyan jami’an da aka saka musu sabbin muƙaman nasu na ƙananan mataimakan Kwanturola Janar akwai ACG Kemi Nandap, babbar jami’ar da ke kula da shige da fice a Filin Jiragen Sama na Murtala Muhammad da ke Legas, da babban jami’in harkokin ofishin CGI da aka sauya kwanan nan, ACG Ahmad Bauchi Aliyu da kuma Kwanturola Mustapha Ahmad, mataimaki na musamman ga CGI a fannin gudanar da ayyuka.

A halin da ake ciki kuma, Ministan Cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola a ranar Talata ya sanya wa sababbin jami’ai da aka naxa a matsayin manyan mataimakan Kwanturola Janar muƙamansu, a babban xakin taro na ma’aikatar. Waxanda aka yi wa ado da muƙaman sun haxa da DCG Oluremi Talabi, DCG Josephine Kwazu, DCG Modupe Anyalechi da kuma DCG Muhammad Aminu Muhammad.

NIS

Ministan ya taya su murna a kan sabbin muƙaman nasu kana ya nemi su yi amfani da basirarsu da ƙwarewar aiki wajen yaƙi da rashin tsaro a ƙasar nan.

Daga cikin manyan mutanen da suka halarci bikin maƙala sabbin muƙaman na NIS akwai Kwamishinan Tarayya na Hukumar Gudanarwa ta CDCFIB, ACG Ado Jaffaru (mai ritaya), da Sanata Uba Sani, da Sakataren Gwamnatin Jihar Kaduna, Malam Bala Abbas Lawal, da wakilan shugabannin rundunonin da ke ƙarƙashin ma’aikatar cikin gida da sauransu.

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gaza
Manyan Labarai

Trump Da Al-Sisi Za Su Jagoranci Taron Zaman Lafiya Dawwamammiya Ta Gaza A Masar

October 12, 2025
‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutum Dubu 100 Tare Da Tarwatsa Mutane Miliyan 2 —Irabor
Manyan Labarai

Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor

October 12, 2025
Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa
Labarai

Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa

October 12, 2025
Next Post
NIS

Gwamnatin Tarayya Ta Samu Naira Biliyan 19.2 Daga Fannin Zinare A Kwatar Shekara

LABARAI MASU NASABA

Kishi

Tsokaci A Kan Mata Masu Tsananin Kishi

October 12, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

October 12, 2025
Gaza

Trump Da Al-Sisi Za Su Jagoranci Taron Zaman Lafiya Dawwamammiya Ta Gaza A Masar

October 12, 2025
Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

October 12, 2025
‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutum Dubu 100 Tare Da Tarwatsa Mutane Miliyan 2 —Irabor

Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor

October 12, 2025
Yadda Ake Gurasa Ta Semovita

Yadda Ake Gurasa Ta Semovita

October 12, 2025
Daga Karshe Tawagar Super Eagles Ta Sauka A Uyo Bayan Saukar Gaggawa A Angola

Daga Karshe Tawagar Super Eagles Ta Sauka A Uyo Bayan Saukar Gaggawa A Angola

October 12, 2025
Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa

Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa

October 12, 2025
Ko Afirka Za Ta Samu Kujerar Dindindin A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Dinkin Duniya?

Ko Afirka Za Ta Samu Kujerar Dindindin A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Dinkin Duniya?

October 12, 2025
Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 

Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 

October 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.