• English
  • Business News
Saturday, October 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Za Ta Sayo Jirage Masu Sarrafa Kansu Don Aikin Sintiri A Iyakokin Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
NIS

Mukaddashiyar Kwanturola Janar ta hukumar kula da shige da fice ta kasa (NIS), Caroline Wuraola Adepoju, ta ce hukumar za ta sayi kananan jiragen sama da jirage masu saukar Angulu da kuma jirage masu sarrafa kansu wato don gudanar da sintirin tsaro a iyakokin kasar nan. 

Caroline ta ce hakan zai taimaka wa hukumar wajen sauke nauyin da aka dora mata, musamman wajen sa ido akan zirga-jirgar jama’a na shige da fice a iyakokin kasar, har a ta hanyar ruwa.

  • Ina Son Ci Gaba Da Zama Kyaftin Din Ingila Har Zuwa 2028 – Harry Kane
  • Jirgin Sojoji Ya Yi Wa ‘Yan Ta’adda Luguden Wuta A Zamfara

Ta bayyana hakan a Legas a taron bita da hukumar ta shirya a rundunar hukumar da ke filin jirgin sama na Murtala Muhammed da ke a jihar.

Kazalika ta ce, wadannan kayan aikin da za a siya, tuni an sanya su a cikin kasafin kudi na 2024 na ma’aikarar kula da harkokin cikin gida.

Bugu da kari, baya ga sayen wadannan kayan aikin, ta ce hukumar na kuma kan ci gaba da zuba jari a fannin kimiyya domin sarrafa takardun tafiye-tafiya da kuma sauran tsare-tsare don kara bunkasa tsaro a iyakokin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari

A cewarta, daga shekara mai zuwa, hukumar za ta tura kofofi masu aikin da wutar lantarki a filayen jiragen sama na kasar don a sauwake wa fasinjoji shiga da fita daga cikin kasar.

Bugu da kari ta yi nuni da cewa, wannan ya nuna kokarin da ministan kula da harkokin cikin gida Dakta Olubunmi Tunji Ojo ke yi akan ajandarsa ta kara tabbatar da tsaro a iyakokin Nijeriya.

A na sa jawabin, Mista Fela Durotoye sabon babban mai taimaka wa na musamman ga shugaban kasa akan darajar kasa da yin adalci, ya shawarci hukumomin da ke aiki a filin jirgin da su hada hannu don su samar da bayanan sirri akan kokarin fa kasar ke yi, na bunkasa tattalin arzikin kasar.

Ita kuwa Kwantirolar rundunar ta filin jirgin uwargida Adeola Adesokan ta bayyana cewa, hada karfe da karfe a tsakanin jami’an tsaro da mahukuntan da ke sa ido a iyakokin kasar, hakan ya kara taimaka wa wajen samun karin masu zuba jari a cikin tattalin arzikin Nijeriya.

Kazalika, Manajin Darakta na hukumar jiragen sama ta kasa Kabir Yusuf ya bayyana cewa, hada karfi da karfe a tsakanin hukumomin na ci gaba da amfanarsu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
Gwamnatin Bauchi Ta Kori Shugaban Kungiyar Kwallon Kafa Ta Wikki Tourist

Gwamnatin Bauchi Ta Kori Shugaban Kungiyar Kwallon Kafa Ta Wikki Tourist

LABARAI MASU NASABA

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa

Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa

October 11, 2025
Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari

Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari

October 11, 2025
Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia

Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia

October 11, 2025
Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa

Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi

Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi

October 11, 2025
Gwamna Aliyu Ya Tsige Hakimai 15 Na Sokoto

A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu – Jama’ar Sakkwato

October 11, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno

October 11, 2025
Ta’addanci

Sojoji Sun Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Lalata Kayayyakin Gwamnati A Binuwe

October 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.