• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Za Ta Sayo Jirage Masu Sarrafa Kansu Don Aikin Sintiri A Iyakokin Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
NIS Za Ta Sayo Jirage Masu Sarrafa Kansu Don Aikin Sintiri A Iyakokin Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mukaddashiyar Kwanturola Janar ta hukumar kula da shige da fice ta kasa (NIS), Caroline Wuraola Adepoju, ta ce hukumar za ta sayi kananan jiragen sama da jirage masu saukar Angulu da kuma jirage masu sarrafa kansu wato don gudanar da sintirin tsaro a iyakokin kasar nan. 

Caroline ta ce hakan zai taimaka wa hukumar wajen sauke nauyin da aka dora mata, musamman wajen sa ido akan zirga-jirgar jama’a na shige da fice a iyakokin kasar, har a ta hanyar ruwa.

  • Ina Son Ci Gaba Da Zama Kyaftin Din Ingila Har Zuwa 2028 – Harry Kane
  • Jirgin Sojoji Ya Yi Wa ‘Yan Ta’adda Luguden Wuta A Zamfara

Ta bayyana hakan a Legas a taron bita da hukumar ta shirya a rundunar hukumar da ke filin jirgin sama na Murtala Muhammed da ke a jihar.

Kazalika ta ce, wadannan kayan aikin da za a siya, tuni an sanya su a cikin kasafin kudi na 2024 na ma’aikarar kula da harkokin cikin gida.

Bugu da kari, baya ga sayen wadannan kayan aikin, ta ce hukumar na kuma kan ci gaba da zuba jari a fannin kimiyya domin sarrafa takardun tafiye-tafiya da kuma sauran tsare-tsare don kara bunkasa tsaro a iyakokin Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

A cewarta, daga shekara mai zuwa, hukumar za ta tura kofofi masu aikin da wutar lantarki a filayen jiragen sama na kasar don a sauwake wa fasinjoji shiga da fita daga cikin kasar.

Bugu da kari ta yi nuni da cewa, wannan ya nuna kokarin da ministan kula da harkokin cikin gida Dakta Olubunmi Tunji Ojo ke yi akan ajandarsa ta kara tabbatar da tsaro a iyakokin Nijeriya.

A na sa jawabin, Mista Fela Durotoye sabon babban mai taimaka wa na musamman ga shugaban kasa akan darajar kasa da yin adalci, ya shawarci hukumomin da ke aiki a filin jirgin da su hada hannu don su samar da bayanan sirri akan kokarin fa kasar ke yi, na bunkasa tattalin arzikin kasar.

Ita kuwa Kwantirolar rundunar ta filin jirgin uwargida Adeola Adesokan ta bayyana cewa, hada karfe da karfe a tsakanin jami’an tsaro da mahukuntan da ke sa ido a iyakokin kasar, hakan ya kara taimaka wa wajen samun karin masu zuba jari a cikin tattalin arzikin Nijeriya.

Kazalika, Manajin Darakta na hukumar jiragen sama ta kasa Kabir Yusuf ya bayyana cewa, hada karfi da karfe a tsakanin hukumomin na ci gaba da amfanarsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ina Son Ci Gaba Da Zama Kyaftin Din Ingila Har Zuwa 2028 – Harry Kane

Next Post

Gwamnatin Bauchi Ta Kori Shugaban Kungiyar Kwallon Kafa Ta Wikki Tourist

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

1 hour ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

2 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

3 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

4 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

6 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

8 hours ago
Next Post
Gwamnatin Bauchi Ta Kori Shugaban Kungiyar Kwallon Kafa Ta Wikki Tourist

Gwamnatin Bauchi Ta Kori Shugaban Kungiyar Kwallon Kafa Ta Wikki Tourist

LABARAI MASU NASABA

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

August 25, 2025
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.