• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Za Ta Sayo Jirage Masu Sarrafa Kansu Don Aikin Sintiri A Iyakokin Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
NIS

Mukaddashiyar Kwanturola Janar ta hukumar kula da shige da fice ta kasa (NIS), Caroline Wuraola Adepoju, ta ce hukumar za ta sayi kananan jiragen sama da jirage masu saukar Angulu da kuma jirage masu sarrafa kansu wato don gudanar da sintirin tsaro a iyakokin kasar nan. 

Caroline ta ce hakan zai taimaka wa hukumar wajen sauke nauyin da aka dora mata, musamman wajen sa ido akan zirga-jirgar jama’a na shige da fice a iyakokin kasar, har a ta hanyar ruwa.

  • Ina Son Ci Gaba Da Zama Kyaftin Din Ingila Har Zuwa 2028 – Harry Kane
  • Jirgin Sojoji Ya Yi Wa ‘Yan Ta’adda Luguden Wuta A Zamfara

Ta bayyana hakan a Legas a taron bita da hukumar ta shirya a rundunar hukumar da ke filin jirgin sama na Murtala Muhammed da ke a jihar.

Kazalika ta ce, wadannan kayan aikin da za a siya, tuni an sanya su a cikin kasafin kudi na 2024 na ma’aikarar kula da harkokin cikin gida.

Bugu da kari, baya ga sayen wadannan kayan aikin, ta ce hukumar na kuma kan ci gaba da zuba jari a fannin kimiyya domin sarrafa takardun tafiye-tafiya da kuma sauran tsare-tsare don kara bunkasa tsaro a iyakokin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

A cewarta, daga shekara mai zuwa, hukumar za ta tura kofofi masu aikin da wutar lantarki a filayen jiragen sama na kasar don a sauwake wa fasinjoji shiga da fita daga cikin kasar.

Bugu da kari ta yi nuni da cewa, wannan ya nuna kokarin da ministan kula da harkokin cikin gida Dakta Olubunmi Tunji Ojo ke yi akan ajandarsa ta kara tabbatar da tsaro a iyakokin Nijeriya.

A na sa jawabin, Mista Fela Durotoye sabon babban mai taimaka wa na musamman ga shugaban kasa akan darajar kasa da yin adalci, ya shawarci hukumomin da ke aiki a filin jirgin da su hada hannu don su samar da bayanan sirri akan kokarin fa kasar ke yi, na bunkasa tattalin arzikin kasar.

Ita kuwa Kwantirolar rundunar ta filin jirgin uwargida Adeola Adesokan ta bayyana cewa, hada karfe da karfe a tsakanin jami’an tsaro da mahukuntan da ke sa ido a iyakokin kasar, hakan ya kara taimaka wa wajen samun karin masu zuba jari a cikin tattalin arzikin Nijeriya.

Kazalika, Manajin Darakta na hukumar jiragen sama ta kasa Kabir Yusuf ya bayyana cewa, hada karfi da karfe a tsakanin hukumomin na ci gaba da amfanarsu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447
Labarai

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Labarai

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025
Sabbin Ministoci
Labarai

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025
Next Post
Gwamnatin Bauchi Ta Kori Shugaban Kungiyar Kwallon Kafa Ta Wikki Tourist

Gwamnatin Bauchi Ta Kori Shugaban Kungiyar Kwallon Kafa Ta Wikki Tourist

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025
Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025
Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

October 21, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

October 21, 2025
Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.