• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NLC Na Zargin Gwamnatin Nijeriya Da Shirya Kai Wa ‘Ya’yanta Hari Yayin Zanga-zangar Yunwa

by Muhammad
1 year ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Dalibai Sun Bukaci Tinubu Da Gwamnoni Da Su Kula Da Sha’anin Tsaro, Ilimi Da Wutar Lantarki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani labari da BBC Hausa ta wallafa a shafinta ya ce, Kungiyar Ƙwadado ta Nijeriya NLC, ta zargi gwamnatin ƙasar da kitsa kai wa ‘ya’yanta hari a lokacin zanga-zangar da ƙungiyar ta shirya gudanarwa a faɗin ƙasar a ranakun 27 da 28 ga watan da muke ciki.

Cikin wata sanarwar da ƙungiyar ta fitar mai ɗauke da sa hannun shugabanta na ƙasa, Comrade Joe Ajaero, NLC ta zargi gwamnatin ƙasar da shirya amfani da wata ƙungiyar farar hula mai suna ‘Nigeria Civil Society Forum’ (NCSF), wajen kai wa ‘ya’yanta hari a lokacin zanga-zangar lumanar da ta shirya gudanarwa.

  • Kungiyar Kwadago (NLC) Na Shirin Tsunduma Wani Sabon Yajin Aiki Mai Dogon Zango
  • NLC Na Neman A Biya Ma’aikata Naira Miliyan Ɗaya A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashi

”NCSF na ɗaya daga cikin ƙungiyoyin da gwamnati ta ɗauki nauyinsu, kuma za ta yi amfani da su don kawo cikas ga zanga-zangar lumana da ‘ya’yan ƙungiyarmu suka shirya don nuna adawa da yunwar da ƙasarmu ke ciki”, in ji Comrade Ajaero.

Ƙungiyar ta ce tana son gwamnati ta fahimci cewa zalunci kan ‘ya’yanta ba shi ne zai yi maganin halin matsin tattalin arziki da yunwa da ƙasar ke ciki ba.

”Kamar yadda gwamnati ta yi a Minna da wasu biranen ƙasar, inda ta riƙa harba hayaƙi mai sai ƙwalla da dukan mata tare da kulle su, kawai don sun nuna damuwarsu kan yunwar da ke damunsu. Bai kamata a ɗauki nauyin wasu don hana mutane bayyana abin da ke damunsu ba. Bai kamata a tarwatsa waɗanda ke kukan yunwa da alburushi ko hayaƙi mai sa ƙwalla ba”, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

Ƙungiyar ta kuma jaddada aniyarta na gudanar da zanga-zangar da ta shirya yi a faɗin ƙasar a ranakun da ta tsara yinsa.

”A don haka NLC da sauran ƙawayenta za mu gudanar da zanga-zangar da muka shirya yi don nuna adawarmu kan tsadar rayuwa da matsin tattalin arziki da rashin tsaro da ƙasarmu ke fuskanta”, in ji Ajaero.

”A matsayinmu na ‘yan ƙasa, muna da ‘yancin gudanar da zanga-zangar, kuma tarihi na nuna cewa a koyaushe zanga-zangarmu ta lumana ce, sai dai a inda gwamnati ta haddasa hargitsi”, in ji Ajaero.

A baya-bayan nan dai hukumomin ƙasar sun riƙa kira ga ƙungiyar kwadagon ta jingine zanga-zangar da ta shirya gudanarwa kan tsadar rayuwa a ƙasar.

Ko a makon da ya gabata ma hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta yi kira ga ƙungiyar NLCn ta dakatar da zanga-zangar saboda dalilai na tsaro.

Haka shi ma ministan shari’a na ƙasar Lateef Fagbemi, cikin wata wasiƙa da ya aike wa lauyan ƙungiyar kwadagon, Femi Falana, ya yi kira ga ƙungiyar ta jingine zanga-zangar da ta shirya yi a faɗin ƙasar.

To sai dai a cikin wasiƙar martani da lauyan ya aike wa ministan ya buƙace shi da samar da jami’an tsaron da za su bai wa ‘ya’yan ƙungiyar kariya a lokacin zanga-zangar lumanar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Game Da Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Sun Nuna Yadda Kasar Ta Samu Ci Gaba Mai Inganci

Next Post

Tsadar Rayuwa: Sojoji Sun Ƙaryata Jita-jitar Shirin Yi Wa Shugaba Tinubu Juyin Mulki

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

39 minutes ago
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa
Manyan Labarai

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

55 minutes ago
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
Manyan Labarai

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

5 hours ago
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…
Manyan Labarai

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

6 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

16 hours ago
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo

1 day ago
Next Post
Tsadar Rayuwa: Sojoji Sun Ƙaryata Jita-jitar Shirin Yi Wa Shugaba Tinubu Juyin Mulki

Tsadar Rayuwa: Sojoji Sun Ƙaryata Jita-jitar Shirin Yi Wa Shugaba Tinubu Juyin Mulki

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

July 11, 2025
Goron Sallah

GORON JUMA’A

July 11, 2025
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

July 11, 2025
Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

July 11, 2025
Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

July 11, 2025
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

July 11, 2025
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

July 11, 2025
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.