• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NLC Na Zargin Gwamnatin Nijeriya Da Shirya Kai Wa ‘Ya’yanta Hari Yayin Zanga-zangar Yunwa

by Muhammad
2 years ago
NLC

Wani labari da BBC Hausa ta wallafa a shafinta ya ce, Kungiyar Ƙwadado ta Nijeriya NLC, ta zargi gwamnatin ƙasar da kitsa kai wa ‘ya’yanta hari a lokacin zanga-zangar da ƙungiyar ta shirya gudanarwa a faɗin ƙasar a ranakun 27 da 28 ga watan da muke ciki.

Cikin wata sanarwar da ƙungiyar ta fitar mai ɗauke da sa hannun shugabanta na ƙasa, Comrade Joe Ajaero, NLC ta zargi gwamnatin ƙasar da shirya amfani da wata ƙungiyar farar hula mai suna ‘Nigeria Civil Society Forum’ (NCSF), wajen kai wa ‘ya’yanta hari a lokacin zanga-zangar lumanar da ta shirya gudanarwa.

  • Kungiyar Kwadago (NLC) Na Shirin Tsunduma Wani Sabon Yajin Aiki Mai Dogon Zango
  • NLC Na Neman A Biya Ma’aikata Naira Miliyan Ɗaya A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashi

”NCSF na ɗaya daga cikin ƙungiyoyin da gwamnati ta ɗauki nauyinsu, kuma za ta yi amfani da su don kawo cikas ga zanga-zangar lumana da ‘ya’yan ƙungiyarmu suka shirya don nuna adawa da yunwar da ƙasarmu ke ciki”, in ji Comrade Ajaero.

Ƙungiyar ta ce tana son gwamnati ta fahimci cewa zalunci kan ‘ya’yanta ba shi ne zai yi maganin halin matsin tattalin arziki da yunwa da ƙasar ke ciki ba.

”Kamar yadda gwamnati ta yi a Minna da wasu biranen ƙasar, inda ta riƙa harba hayaƙi mai sai ƙwalla da dukan mata tare da kulle su, kawai don sun nuna damuwarsu kan yunwar da ke damunsu. Bai kamata a ɗauki nauyin wasu don hana mutane bayyana abin da ke damunsu ba. Bai kamata a tarwatsa waɗanda ke kukan yunwa da alburushi ko hayaƙi mai sa ƙwalla ba”, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

Ƙungiyar ta kuma jaddada aniyarta na gudanar da zanga-zangar da ta shirya yi a faɗin ƙasar a ranakun da ta tsara yinsa.

”A don haka NLC da sauran ƙawayenta za mu gudanar da zanga-zangar da muka shirya yi don nuna adawarmu kan tsadar rayuwa da matsin tattalin arziki da rashin tsaro da ƙasarmu ke fuskanta”, in ji Ajaero.

”A matsayinmu na ‘yan ƙasa, muna da ‘yancin gudanar da zanga-zangar, kuma tarihi na nuna cewa a koyaushe zanga-zangarmu ta lumana ce, sai dai a inda gwamnati ta haddasa hargitsi”, in ji Ajaero.

A baya-bayan nan dai hukumomin ƙasar sun riƙa kira ga ƙungiyar kwadagon ta jingine zanga-zangar da ta shirya gudanarwa kan tsadar rayuwa a ƙasar.

Ko a makon da ya gabata ma hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta yi kira ga ƙungiyar NLCn ta dakatar da zanga-zangar saboda dalilai na tsaro.

Haka shi ma ministan shari’a na ƙasar Lateef Fagbemi, cikin wata wasiƙa da ya aike wa lauyan ƙungiyar kwadagon, Femi Falana, ya yi kira ga ƙungiyar ta jingine zanga-zangar da ta shirya yi a faɗin ƙasar.

To sai dai a cikin wasiƙar martani da lauyan ya aike wa ministan ya buƙace shi da samar da jami’an tsaron da za su bai wa ‘ya’yan ƙungiyar kariya a lokacin zanga-zangar lumanar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260
Manyan Labarai

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
gaza
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
Next Post
Tsadar Rayuwa: Sojoji Sun Ƙaryata Jita-jitar Shirin Yi Wa Shugaba Tinubu Juyin Mulki

Tsadar Rayuwa: Sojoji Sun Ƙaryata Jita-jitar Shirin Yi Wa Shugaba Tinubu Juyin Mulki

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025
Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

October 28, 2025
Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

October 28, 2025
gaza

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.