• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NLC Na Zargin Gwamnatin Nijeriya Da Shirya Kai Wa ‘Ya’yanta Hari Yayin Zanga-zangar Yunwa

by Muhammad
1 year ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Dalibai Sun Bukaci Tinubu Da Gwamnoni Da Su Kula Da Sha’anin Tsaro, Ilimi Da Wutar Lantarki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani labari da BBC Hausa ta wallafa a shafinta ya ce, Kungiyar Ƙwadado ta Nijeriya NLC, ta zargi gwamnatin ƙasar da kitsa kai wa ‘ya’yanta hari a lokacin zanga-zangar da ƙungiyar ta shirya gudanarwa a faɗin ƙasar a ranakun 27 da 28 ga watan da muke ciki.

Cikin wata sanarwar da ƙungiyar ta fitar mai ɗauke da sa hannun shugabanta na ƙasa, Comrade Joe Ajaero, NLC ta zargi gwamnatin ƙasar da shirya amfani da wata ƙungiyar farar hula mai suna ‘Nigeria Civil Society Forum’ (NCSF), wajen kai wa ‘ya’yanta hari a lokacin zanga-zangar lumanar da ta shirya gudanarwa.

  • Kungiyar Kwadago (NLC) Na Shirin Tsunduma Wani Sabon Yajin Aiki Mai Dogon Zango
  • NLC Na Neman A Biya Ma’aikata Naira Miliyan Ɗaya A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashi

”NCSF na ɗaya daga cikin ƙungiyoyin da gwamnati ta ɗauki nauyinsu, kuma za ta yi amfani da su don kawo cikas ga zanga-zangar lumana da ‘ya’yan ƙungiyarmu suka shirya don nuna adawa da yunwar da ƙasarmu ke ciki”, in ji Comrade Ajaero.

Ƙungiyar ta ce tana son gwamnati ta fahimci cewa zalunci kan ‘ya’yanta ba shi ne zai yi maganin halin matsin tattalin arziki da yunwa da ƙasar ke ciki ba.

”Kamar yadda gwamnati ta yi a Minna da wasu biranen ƙasar, inda ta riƙa harba hayaƙi mai sai ƙwalla da dukan mata tare da kulle su, kawai don sun nuna damuwarsu kan yunwar da ke damunsu. Bai kamata a ɗauki nauyin wasu don hana mutane bayyana abin da ke damunsu ba. Bai kamata a tarwatsa waɗanda ke kukan yunwa da alburushi ko hayaƙi mai sa ƙwalla ba”, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Labarai Masu Nasaba

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Ƙungiyar ta kuma jaddada aniyarta na gudanar da zanga-zangar da ta shirya yi a faɗin ƙasar a ranakun da ta tsara yinsa.

”A don haka NLC da sauran ƙawayenta za mu gudanar da zanga-zangar da muka shirya yi don nuna adawarmu kan tsadar rayuwa da matsin tattalin arziki da rashin tsaro da ƙasarmu ke fuskanta”, in ji Ajaero.

”A matsayinmu na ‘yan ƙasa, muna da ‘yancin gudanar da zanga-zangar, kuma tarihi na nuna cewa a koyaushe zanga-zangarmu ta lumana ce, sai dai a inda gwamnati ta haddasa hargitsi”, in ji Ajaero.

A baya-bayan nan dai hukumomin ƙasar sun riƙa kira ga ƙungiyar kwadagon ta jingine zanga-zangar da ta shirya gudanarwa kan tsadar rayuwa a ƙasar.

Ko a makon da ya gabata ma hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta yi kira ga ƙungiyar NLCn ta dakatar da zanga-zangar saboda dalilai na tsaro.

Haka shi ma ministan shari’a na ƙasar Lateef Fagbemi, cikin wata wasiƙa da ya aike wa lauyan ƙungiyar kwadagon, Femi Falana, ya yi kira ga ƙungiyar ta jingine zanga-zangar da ta shirya yi a faɗin ƙasar.

To sai dai a cikin wasiƙar martani da lauyan ya aike wa ministan ya buƙace shi da samar da jami’an tsaron da za su bai wa ‘ya’yan ƙungiyar kariya a lokacin zanga-zangar lumanar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Game Da Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Sun Nuna Yadda Kasar Ta Samu Ci Gaba Mai Inganci

Next Post

Tsadar Rayuwa: Sojoji Sun Ƙaryata Jita-jitar Shirin Yi Wa Shugaba Tinubu Juyin Mulki

Related

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

16 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

2 days ago
Next Post
Tsadar Rayuwa: Sojoji Sun Ƙaryata Jita-jitar Shirin Yi Wa Shugaba Tinubu Juyin Mulki

Tsadar Rayuwa: Sojoji Sun Ƙaryata Jita-jitar Shirin Yi Wa Shugaba Tinubu Juyin Mulki

LABARAI MASU NASABA

Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.