• Leadership Hausa
Monday, May 29, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPP Ta Zargi Gwamnatin Ganduje Da Kai Hare-Hare Kan Mazauna Kano

by Sulaiman
2 months ago
in Labarai
0
DSS Ce Abokiyar Hamayyar Mu A Jihar Kano Ba APC Ba – NNPP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar NNPP ta zargi gwamnatin jihar Kano da kai hare-hare kan mutanen da ba su ji ba su gani ba bayan ayyana Abba Kabir Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna na 2023 da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta yi.

 

Jam’iyyar a cikin wata sanarwa da ta fito daga shugabanta na jihar, Hon Umar Haruna Doguwa, ta ce wasu ‘yan daba da ake zargin gwamnatin jihar ce ta dauki nauyinsu sun ba da umarnin kai hare-hare a wurare daban-daban a cikin birnin jihar.

  • Ba Za Mu Bari NNPP Ta Yi Magudin Zabe A Kano Ba —Gwamnatin Kano

Sanarwar ta ce jam’iyyar NNPP ta nuna takaicinta kan salon APC na yadda take nuna damuwarta kan rashin nasarar lashe zaben gwamna a 2023.

“Mutanen Kano za su iya tuna cewa bayan ‘yan mintoci kadan da bayyana nasararmu mai dimbin tarihi, zababben gwamnan NNPP Abba Kabir Yusuf ta bakin mai magana da yawunsa, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar da sanarwa inda ya bukaci daukacin magoya bayansa da su gudanar da murnarsu cikin lumana a yayin bukukuwan nasarar jam’iyyar, yayin da ni kaina a matsayina na shugaban NNPP na jihar na kasance a gidajen rediyo daban-daban ina kara kira kan hakan, kuma magoya bayanmu sun bi umarninmu amma ‘yan daban jam’iyyar adawa sun fara kai hare-hare ga mutanenmu.

Labarai Masu Nasaba

Da Dumi-dumi: An Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Nijeriya Na 16

A Dan Lokacin Da Ya Rage Kafin Mika Mulki: Buhari Ya Sauya Sunayen Filayen Jiragen Sama 15

 

“Jam’iyyar NNPP tana da sahihan bayanai cewa, gwamnatin jihar na sake shirya wani tashin hankali da sunan zanga-zangar adawa da INEC da jami’an tsaro da ke aiki a Kano kan rashin nasarar APC a zaben gwamna da aka kammala.

 

“A halin yanzu mun samu labarin ana tattara motoci 50 na ‘yan daba daga kowace karamar hukuma 44 da nufin lalata dukiyoyin jama’a da cibiyoyin INEC a fadin jihar. Shirin shi ne a yi amfani da jar hular Kwankwasiyya wajen aikata wannan mummunan aikin.”

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zan Yi Mulki Da Kowa, Zan Rike Amanar Al’ummar Jihar Kaduna – Uba Sani

Next Post

Mata Magoya Bayan PDP Na Zanga-Zangar Watsi Da Sakamakon Zaben Gwamnan Kaduna

Related

Da Dumi-dumi: An Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Nijeriya Na 16
Labarai

Da Dumi-dumi: An Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Nijeriya Na 16

1 hour ago
A Dan Lokacin Da Ya Rage Kafin Mika Mulki: Buhari Ya Sauya Sunayen Filayen Jiragen Sama 15
Labarai

A Dan Lokacin Da Ya Rage Kafin Mika Mulki: Buhari Ya Sauya Sunayen Filayen Jiragen Sama 15

2 hours ago
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 
Labarai

Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

2 hours ago
Bankwana Da Gwamnatin Buhari: Hukumar Tsaron Cikin Gida Ta Kara Wa Jami’ai 17,331 Matsayi
Labarai

Bankwana Da Gwamnatin Buhari: Hukumar Tsaron Cikin Gida Ta Kara Wa Jami’ai 17,331 Matsayi

3 hours ago
Kwana Guda Ya Sauka, El-Rufai Ya Haramta Kungiyar Kudancin Kaduna
Labarai

Kwana Guda Ya Sauka, El-Rufai Ya Haramta Kungiyar Kudancin Kaduna

5 hours ago
Buhari Ya Nada Sha’aban Mukamin Babban Sakataren Hukumar Kula Da Almajirai Ta Nijeriya
Labarai

Buhari Ya Nada Sha’aban Mukamin Babban Sakataren Hukumar Kula Da Almajirai Ta Nijeriya

12 hours ago
Next Post
Mata Magoya Bayan PDP Na Zanga-Zangar Watsi Da Sakamakon Zaben Gwamnan Kaduna

Mata Magoya Bayan PDP Na Zanga-Zangar Watsi Da Sakamakon Zaben Gwamnan Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Da Dumi-dumi: An Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Nijeriya Na 16

Da Dumi-dumi: An Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Nijeriya Na 16

May 29, 2023
A Dan Lokacin Da Ya Rage Kafin Mika Mulki: Buhari Ya Sauya Sunayen Filayen Jiragen Sama 15

A Dan Lokacin Da Ya Rage Kafin Mika Mulki: Buhari Ya Sauya Sunayen Filayen Jiragen Sama 15

May 29, 2023
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

May 29, 2023
Bankwana Da Gwamnatin Buhari: Hukumar Tsaron Cikin Gida Ta Kara Wa Jami’ai 17,331 Matsayi

Bankwana Da Gwamnatin Buhari: Hukumar Tsaron Cikin Gida Ta Kara Wa Jami’ai 17,331 Matsayi

May 29, 2023
Gwamnati Ta Samar Da Tan 89,512 Na Irin Noma A Bana – Minista

Gwamnati Ta Samar Da Tan 89,512 Na Irin Noma A Bana – Minista

May 29, 2023
Kwana Guda Ya Sauka, El-Rufai Ya Haramta Kungiyar Kudancin Kaduna

Kwana Guda Ya Sauka, El-Rufai Ya Haramta Kungiyar Kudancin Kaduna

May 29, 2023
Buhari Ya Nada Sha’aban Mukamin Babban Sakataren Hukumar Kula Da Almajirai Ta Nijeriya

Buhari Ya Nada Sha’aban Mukamin Babban Sakataren Hukumar Kula Da Almajirai Ta Nijeriya

May 28, 2023
An Wallafa Littafin Dake Kunshe Da Mukalolin Shugaba Xi Kan Dogaro Da Kai A Fannin Kimiyya Da Fasaha

An Wallafa Littafin Dake Kunshe Da Mukalolin Shugaba Xi Kan Dogaro Da Kai A Fannin Kimiyya Da Fasaha

May 28, 2023
Ganduje Yayi Jawabin Bankwana Tare Da Shirin Mika Mulki A Yau Lahadi

Ganduje Yayi Jawabin Bankwana Tare Da Shirin Mika Mulki A Yau Lahadi

May 28, 2023
Jihar Kano Ta Ayyana Masu Kwacen Waya A Matsayin ‘Yan Fashi Da Makami

Jihar Kano Ta Ayyana Masu Kwacen Waya A Matsayin ‘Yan Fashi Da Makami

May 28, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.