ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

by Abubakar Abba
6 months ago
Noma

A makwannin da suka gabata, yankuna da dama na kasar nan, sun samu ruwan sama kamar da bakin kwarya. Hukumar kula da yanayi ta kasa (NiMet), a ranar 4 ga watan Fabrairun 2025, ta kaddamar da kundin hasashe kan yadda yanayi zai kasance a kakar noman shekarar 2025.

Kundin ya yi hasashen cewa, za a samu ruwan sama kamar da bakin kwarya a wannan shekara da muke ciki (bana), wanda ruwan saman, mai yiwuwa zai sauka da wuri a shekarar 2025 din.

Tuni dai, kamar yadda dai aka saba, wasu manoma a kasar duk da cewa, daminar kakar 2025 din ba ta riga ta kankama ba, suka fara yin shuka a gonakinsu.

ADVERTISEMENT
  • Radda Ya Raba Wa Manoma Taki A Jihar Katsina
  • Sabbin Fasahohin Noma Na Zamani Na Ci Gaba Da Bayyana A Kasar Sin

Misali, rahotannin sun bayyana cewa, a Kananan Hukumomin Akwanga, Lafia da Doma da ke Jihar Nasarawa, sun shuka Irin gyada kawai domin sa ran samun ruwan sama a makon da ya gabata, wanda hakan ya sanya yanzu suke jin tsoro ganin cewa, ba a sake yin wani ruwan saman ba, hakan ya kuma sanya Irin gyadar da suka shuka, zafin rana ya fara lalata shi.

Haka nan ma, batun yake a babban birnin tarayyar Abuja, kamar yadda wasu rahotanni suka bayyana, musamman ga wasu  manoman da ke zaune a wasu sassa na Bwari da kuma wasu kauyuka da ke makwabtaka da Jihar Neja, da suka yi hanzarin yin shuka, su ma suka shiga cikin fargaba ta rashin samun sake saukar ruwan na sama.

LABARAI MASU NASABA

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

Bugu da kari, wasu kwararru a fannin aikin noma, su ma tuni suka gargadi manoman kan kaucewa yin shuka da wuri, inda suka shawarce su da su tabbatar da sun kiyaye da hasashen na hukumar ta NiMet, domin kaucewa tabka asara da kuma yin da-na-sani.

Lokacin Da Ya Fi Dacewa Manona Su Yi Shuka:

Wata kungiya mai bayar da agajin gaggawa, (Christian Aids) tare da hadaka da wasu abokan hudda, sun samar da wata taswira da ke kunshe da lokacin da ya fi dacewa manoman da ke jihohin kasar 36 ciki har da babban birnin tarayayyar Abuja, su yi shuka.

Taswirar wadda ta kasance mai saukin amfanai, sun tsara matakan da suka kamata manoman su bi, na kiyaye lokacin yin shuka, mussamman domin manoman su kauce wa fadawa cikin matsalar irin yadda suka tsinci kansu a ciki a kakar noman shekarar 2024.

Idan za a iya tunawa, hukumar ta NiMet, a wasu bayanai da ta wallafa na farko da suka kuma karade shafukan sada zumunta na zamani a 2025, ta sanar da manoman kasar, ranakun da ya kamata su fara yin shuka da kuma Irin da ya kamata su shuka.

Kazalika, hukumar ta kuma shawarci manoman da su gujewa yin shuka da wuri, duba da bayanan sauyin yanayi da hukumar ta yi hasashen za a iya samu a kasar.

Idan za a iya tunawa, a kakar noma ta shekarar 2024, wasu manoman kasar da dama da suka yi shuka da wuri, sun tabka mummunar asara.

Wani malamain gona mai suna Jacob Auta, ya shawarci manoman kasar cewa; kada su yi saurin yin shuka, inda ya kara da cewa; duba da yadda Irin noma ya yi tsada, ya zama wajibi manoman su sanya ido kafin su fara yin shuka.

Ya yi nuni da cewa, wasu daga cikin Irin noman, ba sa iya jurewa yanayi kamar na zafi, idan an shuka su.

Jacob ya kara da cewa, idan har manoman sun yi shuka kuma ya kasance an kai sama da mako daya ba a samu ruwan sama ba, za su iya tafka asara.

“Haka nan, batun yake a kan sauran amfanin gona, sai dai kawai idan manomi, yana da kayan ban ruwan da zai iya rika yi wa gonarsa ban ruwa,”  in ji Jacob.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Noma Da Kiwo

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Next Post
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

November 11, 2025
CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

November 11, 2025
Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

November 11, 2025
CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

November 11, 2025
Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.