• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

by Rabi'u Ali Indabawa
4 hours ago
in Labarai
0
NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakataren Zartarwa na Hukumar Kula da Jami’o’i ta Kasa (NUC), Farfesa Abdullahi Yusuf Ribadu, ya bukaci jami’o’in Nijeriya da su rungumi kirkire-kirkire domin dacewa a wannan karni na 21, yana mai jaddada cewa dole ne jami’o’i su tashi daga zama jami’o’in da ke ba da digiri na farko su zama jiga-jigan kere-kere da fasaha da ci gaban kasa.

Farfesa Ribadu ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake gabatar da sakon fatan alheri a taron jama’a karo na hudu na Makarantar Tattalin Arziki ta Afirka (ASE), Abuja, wanda Farfesa Moses Ochonu na Jami’ar Banderbilt ta Amurka ya gabatar.

  • Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
  • Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Babban Sakatare, wanda Daraktan ci gaban fasaha da kasuwanci na NUC, Mista Ashafa Ladan, ya wakilta, ya bayyana cewa jami’o’in Nijeriya na karni na 21, “kamar Makarantar Koyon Tattalin Arziki ta Afirka, Jami’ar Pan-African of Edcellence, dole ne su sha bamban da na magabata na karni na 20, yana mai karawa da cewa dole ne su zama “cibiyar bullo da sabbin dabaru da warware matsalolin duniya.”

Farfesa Ribadu ya ce waDanda suka kammala karatun jami’o’in Nijeriya “dole ne su kasance masu nutsuwa, masu sana’a, da kuma da’a yayin da binciken da ke fitowa daga jami’o’i, ba wai kawai su sanar da binciken ba, har ma su ba da gudummawa ga ci gaban kasa, ci gaban fasaha da kyautata zamantakewa.

A cikin sakon fatan alherinsa, Sakatare-Janar na Kwamitin Mataimakin Shugaban Jami’o’in Nijeriya (CBCNU), Farfesa Andrew Haruna, ya yaba wa Mataimakin Shugaban ASE, Farfesa Mahfouz Adedimeji da ma’aikatar don “yunkurinsu na ci gaba da bunkasa ilimi.”

Labarai Masu Nasaba

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

Abba Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe A Jihar Kano

Ya yi nuni da cewa, jami’o’i na cikin tsaka mai wuya wajen samun sauye-sauye a duniya cikin sauri da kuma bukatu na cikin gida, wanda ke bukatar lallai sai sun sake yin nazari sosai kan tsarinsu, da dabi’unsu, domin samar da ingantaccen muradun al’ummarmu da nahiyarmu.

Ya kuma jaddada mahimmancin hangen nesa inda jami’o’i za su zama matattarar kirkire-kirkire, masu inganci da kawo sauyi a zamantakewar al’umma.

“Bari in yaba wa Makarantar Tattalin Arziki ta Afirka saboda himma da hangen nesa, ASE ta riga ta nuna kyakkyawar manufa wajen inganta karfin matasan Afirka da daidaita manyan makarantu tare da bukatun juyin-juya halin masana’antu na hudu,” in ji shi.

A cikin laccarsa mai taken, “Jami’ar Nijeriya ta Karni na 21: Matsaloli da Hanyoyi”, Babban Bako mai jawabi, Farfesa Ochonu, ya bukaci jami’o’in Nijeriya da su rungumi sauye-sauye, hade da bangarori daban-daban da kuma kusantar ilimantarwa don ci gaba da kasancewa masu dacewa a cikin kalubalen karni na 21.

A cewarsa, jami’o’i a duk fadin duniya suna fuskantar kalubale da yawa yayin da tattalin arzikin duniya ke rugujewa a karkashin tasirin juyin juya halin fasaha da na dijital a cikin ilimi, bincike da koyo. Jami’o’in Nijeriya, in ji shi, ba a cire su daga wadannan matsi ba.

Farfesa Ochonu ya yi Allah wadai da rushewar ka’idojin ilimi mai zurfi a wasu jami’o’in gwamnati wanda hakan ya sanya su zama “appendages of parochial serbices of edclusibity” yana mai cewa ana maye gurbin ilimin jama’a ta hanyar ilimin kimiyya.

Yayin da yake tabbatar da cewa fafutukar da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta yi ta tsawon shekaru ta samu wasu muhimman mutane a wuraren aiki na ilimi, ya kuma bayyana cewa gwagwarmayar ta kuma zama wani bangare na matsalar, inda ya kara da cewa “malamai da dama na ci gaba da tsallake karatu, rashin kulawa da horar da daliban jami’o’i da dama sun dage, ba a ci gaba da koyar da dalibai da yawa.”

Ya ba da shawarar Dokar Hakkin dalibi don kare dalibai a cikin alakar ilimi, kulawa, da jagoranci tare da malamai.

Farfesa Ochonu ya kuma ba da kwarin guiwa wajen sabunta sana’ar koyarwa, inda ya jaddada cewa kamata ya yi jami’o’i su kafa cibiyoyin koyarwa da kuma bayar da lambobin yabo don nagartar koyarwa domin inganta koyarwa.

Malamin da ya lashe lambar yabo ya kuma bayar da shawarar samar da tsarin da zai bai wa kwararru da ma’aikata a cikin al’umma damar samun sabbin fasahohi, kwarewa a fannoni masu tasowa da kuma gamsar da sha’awarsu ta hanyar yin rajista guda daya tare da jaddada bukatar sake fasalin manhaja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NUC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA

Next Post

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

Related

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

59 minutes ago
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa
Labarai

Abba Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe A Jihar Kano

2 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

2 hours ago
Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari
Labarai

Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari

3 hours ago
Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA
Labarai

Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA

5 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

5 hours ago
Next Post
Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

LABARAI MASU NASABA

Lardin Hainan Na Kasar Sin Ya Samu Karuwar Cinikayyar Hajoji Da Aka Daukewa Haraji Cikin Shekaru Biyar

Lardin Hainan Na Kasar Sin Ya Samu Karuwar Cinikayyar Hajoji Da Aka Daukewa Haraji Cikin Shekaru Biyar

July 4, 2025
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

July 4, 2025
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Abba Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe A Jihar Kano

July 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

July 4, 2025
Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari

Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari

July 4, 2025
Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

July 4, 2025
NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

July 4, 2025
Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA

Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA

July 4, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

July 4, 2025

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

July 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.