Sanin kowa ne Amurka ta janye jikinta daga yarjejeniyar nukiliyar Iran a shekarar 2018 bisa radin kanta, abin da ya sabawa ka’idar kasa da kasa. A kwanakin baya kuma, Amurka ta kai hari kan na’urorin nukiliya a kasar Iran, matakin ya illata tsarin hana yaduwar makaman nukiliya da zubar da mutunci da sunanta a duniya.
A ran 22 ga wata, mujallar “The Atlantic” ta kasar Amurka ta ruwaito maganar wani jami’in kawar kasar Amurka, wanda ya taba tattauna da shugaba Donald Trump kan harin, cewa dalilin da ya sa Trump ya yanke shawarar kaiwa Iran harin shi ne, sabo da nasarorin da Isra’ila ta cimma ta kai hare-hare ga Iran sun burge shi, har ya sa ya amince cewa, za a samu karin nasarori idan an dauki matakin nuna karfin tuwo.
Sai dai abin da shugaba Trump ya furta na wai nasarori, mataki ne na cimma burin siyasa ta hanyar tsoma hannu a rikicin dake tsakanin Isra’ila da Iran bisa fifikonta na karfin soja, matakin ya sabawa kokarin da ake yi ta hanyar diplomasiyya da ta shawarwari. Ba shakka, nuna karfin tuwo ba zai kawo wa yankin gabas ta tsakiya zaman lafiya ba ko kadan, a maimakon haka, yin shawarwari da juna zai samar da mafita.
Lokacin da yau shugaba Trump ya ambaci yarjejeniyar tsagaita bude wuta a tsakanin Iran da Isra’ila ta kafar sada zumunta, ya jaddada cewa, “kada a keta yarjejeniyar”. Fatanmu a nan shi ne Amurka ita ma za ta nace ga bin ka’idar kasa da kasa, da tabbatar da matakin tsagaita bude wuta tsakanin wadannan bangarorin biyu da kuma cimma hakikanin nasara a shawarawrinsu. (Mai zane da rubutu: MINA)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp