ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Okorocha Ya Musanta Zargin Damfarar N2.9bn, Zai Ci Gaba Da Zama A Hannun EFCC

by Muhammad
4 years ago
Okorocha

 

A ranar Litinin din da ta gabata ne aka gurfanar da tsohon gwamnan jihar Imo, Sanata Rochas Okorocha a gaban wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, kan zargin damfara.

Tsohon gwamnan ya ki amsa tuhumar da ake masa kan cin hanci da rashawa na zabar kudi N2.9bn da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) take tuhumarsa.

ADVERTISEMENT
  • Zaben Fidda Gwani Na PDP: Wike Shi Ne Wanda Ya Yi Nasara —Orji Kalu
  • Yau Litinin APC Za Ta Fara Tantance Masu Neman Takarar Shugaban Ƙasa

A tuhume-tuhume 17, Okorocha ana zarginsa da karkatar da N2.9bn daga asusun gwamnatin jihar Imo da na asusun hadaka na karamar hukumar jihar Imo da kamfanoni masu zaman kansu.

An bayyana cewa Okorocha da wani Anyim Inyerere ne suka yi amfani da kamfanoninsu masu zaman kansu tsakanin shekarar 2014 zuwa 2016 lokacin da yake rike da kujerar gwamnan jihar Imo.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Ko da yake ya musanta dukkan tuhume-tuhumen da ake yi masa, Okorocha, ya dauki manyan lauyoyin Nijeriya hudu da suka hada da Okey Amaechi, Solomon Umor, Ola Olanipekun da Kehinde Ogunwumiju, domin kare shi daga zargin da ake masa.

Jim kadan bayan karbar karar, lauyan EFCC, Gbolahan Latona, ya bukaci alkalin da a dage shari’ar domin ya samu damar hada shaidunsa da za su bayar da shaida yayin shari’a.

Ya shaida wa kotun cewa an shirya shaidu 15 da za su ba da shaida akan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar (APC) kuma akasarin shaidun ba sa hurumin kotun ne saboda kebantattun tuhume-tuhumen.

Lauyan Okorocha, Okey Amaechi, ya shaida wa kotun cewa ya shigar da bukatar naman belin wanda yake karewa, haka kuma ya taba yi wa EFCC.

Ya yi yunkurin yin gardama kan bukatar amma hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta nuna adawa da shi inda ta yi ikirarin cewa tana da niyyar shigar da kara kan bukatar belin.

Ko da yake, lauyan EFCC ya bukaci dage shari’ar zuwa ranar 1 ga watan Yuni, 2022 domin muhawara kan beli, Mai shari’a Ekwo ya yanke hukuncin cewa zai saurari bukatar belinsa a ranar 31 ga Mayu, ya kuma umurci EFCC da ta yi kokarin shigar da karar tata cikin lokaci.

Daga bisani mai shari’a Inyang Ekwo ya bayar da umarnin ci gaba da tsare Okorocha a hukumar EFCC har zuwa ranar 31 ga watan Mayu inda za a yi muhawara kan neman belinsa.

Okorocha
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
  • Muhammad
    ‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
2023: Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar LP, Pat Utomi Ya Janyewa Peter Obi

2023: Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam'iyyar LP, Pat Utomi Ya Janyewa Peter Obi

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.