• Leadership Hausa
Saturday, June 3, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Okorocha Ya Musanta Zargin Damfarar N2.9bn, Zai Ci Gaba Da Zama A Hannun EFCC

by Muhammad
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Okorocha Ya Musanta Zargin Damfarar N2.9bn, Zai Ci Gaba Da Zama A Hannun EFCC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

 

A ranar Litinin din da ta gabata ne aka gurfanar da tsohon gwamnan jihar Imo, Sanata Rochas Okorocha a gaban wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, kan zargin damfara.

Tsohon gwamnan ya ki amsa tuhumar da ake masa kan cin hanci da rashawa na zabar kudi N2.9bn da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) take tuhumarsa.

  • Zaben Fidda Gwani Na PDP: Wike Shi Ne Wanda Ya Yi Nasara —Orji Kalu
  • Yau Litinin APC Za Ta Fara Tantance Masu Neman Takarar Shugaban Ƙasa

A tuhume-tuhume 17, Okorocha ana zarginsa da karkatar da N2.9bn daga asusun gwamnatin jihar Imo da na asusun hadaka na karamar hukumar jihar Imo da kamfanoni masu zaman kansu.

An bayyana cewa Okorocha da wani Anyim Inyerere ne suka yi amfani da kamfanoninsu masu zaman kansu tsakanin shekarar 2014 zuwa 2016 lokacin da yake rike da kujerar gwamnan jihar Imo.

Labarai Masu Nasaba

Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano

Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori

Ko da yake ya musanta dukkan tuhume-tuhumen da ake yi masa, Okorocha, ya dauki manyan lauyoyin Nijeriya hudu da suka hada da Okey Amaechi, Solomon Umor, Ola Olanipekun da Kehinde Ogunwumiju, domin kare shi daga zargin da ake masa.

Jim kadan bayan karbar karar, lauyan EFCC, Gbolahan Latona, ya bukaci alkalin da a dage shari’ar domin ya samu damar hada shaidunsa da za su bayar da shaida yayin shari’a.

Ya shaida wa kotun cewa an shirya shaidu 15 da za su ba da shaida akan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar (APC) kuma akasarin shaidun ba sa hurumin kotun ne saboda kebantattun tuhume-tuhumen.

Lauyan Okorocha, Okey Amaechi, ya shaida wa kotun cewa ya shigar da bukatar naman belin wanda yake karewa, haka kuma ya taba yi wa EFCC.

Ya yi yunkurin yin gardama kan bukatar amma hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta nuna adawa da shi inda ta yi ikirarin cewa tana da niyyar shigar da kara kan bukatar belin.

Ko da yake, lauyan EFCC ya bukaci dage shari’ar zuwa ranar 1 ga watan Yuni, 2022 domin muhawara kan beli, Mai shari’a Ekwo ya yanke hukuncin cewa zai saurari bukatar belinsa a ranar 31 ga Mayu, ya kuma umurci EFCC da ta yi kokarin shigar da karar tata cikin lokaci.

Daga bisani mai shari’a Inyang Ekwo ya bayar da umarnin ci gaba da tsare Okorocha a hukumar EFCC har zuwa ranar 31 ga watan Mayu inda za a yi muhawara kan neman belinsa.

Tags: DamfaraEFCCOkorochaRochas
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Fidda Gwani Na PDP: Wike Shi Ne Wanda Ya Yi Nasara —Orji Kalu

Next Post

2023: Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar LP, Pat Utomi Ya Janyewa Peter Obi

Related

Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano
Manyan Labarai

Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano

6 hours ago
Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori

21 hours ago
Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur
Manyan Labarai

Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur

23 hours ago
Tinubu Ya Nada Akume Da Femi A Sakataren Gwamnati Da Shugaban Ma’aikatan Fadarsa
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Akume Da Femi A Sakataren Gwamnati Da Shugaban Ma’aikatan Fadarsa

1 day ago
Tinubu Ya Nada Dele Alake A Matsayin Mai Magana Da Yawunsa
Manyan Labarai

Tinubu Ya Shiga Wata Ganawa Da Gwamnonin Jam’iyyar APC A Abuja

1 day ago
Cire Tallafin Man Fetur Ba Nan Take Zai Fara Aiki Ba, Sai Karshen Watan Yuni – Tinubu 
Manyan Labarai

Shugaban Nijeriya Na 16: Jan Aikin Da Ke Gaban Jagaban

1 day ago
Next Post
2023: Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar LP, Pat Utomi Ya Janyewa Peter Obi

2023: Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam'iyyar LP, Pat Utomi Ya Janyewa Peter Obi

LABARAI MASU NASABA

Shanuna Sun Fi Saukin Kiwo A Kan Mulkin Nijeriya – Buhari

Shanuna Sun Fi Saukin Kiwo A Kan Mulkin Nijeriya – Buhari

June 3, 2023
Tinubu Ya Nada Dele Alake A Matsayin Mai Magana Da Yawunsa

Abba Gida-Gida Ya Ba Da Umarnin Rushe Gine-Ginen Da Aka Yi A Filayen Gwamnati

June 3, 2023
Sama Da 280 Ne Suka Mutu, 1000 Suka Jikkata A Hatsarin Jirgin Kasa A Indiya

Sama Da 280 Ne Suka Mutu, 1000 Suka Jikkata A Hatsarin Jirgin Kasa A Indiya

June 3, 2023
Alhazan Abuja Sun Gamu Da Tasku Sakamakon Rashin Samun Masaukai Masu Kyau A Saudiyya 

Za Mu Kwashe Daukacin Maniyyatan Bana 6000 – Hukumar Alhazan Kano

June 3, 2023
Kungiyoyin Da Suka Fi Samun Katin Gargadi A Gasar Firimiya Ta Bana

Kungiyoyin Da Suka Fi Samun Katin Gargadi A Gasar Firimiya Ta Bana

June 3, 2023
Ƴan Sanda A Gombe Sun Kama Matasa 11 Da Ake Zargi Da Kalare

Ƴan Sanda A Gombe Sun Kama Matasa 11 Da Ake Zargi Da Kalare

June 3, 2023
Bello Matawalle Ya Wawashe Kudi Da Motocin Gwamnati — Gwamnatin Zamfara

Bello Matawalle Ya Wawashe Kudi Da Motocin Gwamnati — Gwamnatin Zamfara

June 3, 2023
Ci Gaban Al’umma: Ƙungiyar GMBNI Ta Karrama Ma’aikacin LEADERSHIP Da Wasu

Ci Gaban Al’umma: Ƙungiyar GMBNI Ta Karrama Ma’aikacin LEADERSHIP Da Wasu

June 3, 2023
Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano

Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano

June 3, 2023
Duk Ɗan Siyasar Da Ya Shiga Rigar Kwankwaso Ya Kauce Hanya Zai Gani A 2027 – Alhaji Ibrahim

Duk Ɗan Siyasar Da Ya Shiga Rigar Kwankwaso Ya Kauce Hanya Zai Gani A 2027 – Alhaji Ibrahim

June 3, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.