ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Okorocha Ya Musanta Zargin Damfarar N2.9bn, Zai Ci Gaba Da Zama A Hannun EFCC

by Muhammad
4 years ago
Okorocha

 

A ranar Litinin din da ta gabata ne aka gurfanar da tsohon gwamnan jihar Imo, Sanata Rochas Okorocha a gaban wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, kan zargin damfara.

Tsohon gwamnan ya ki amsa tuhumar da ake masa kan cin hanci da rashawa na zabar kudi N2.9bn da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) take tuhumarsa.

ADVERTISEMENT
  • Zaben Fidda Gwani Na PDP: Wike Shi Ne Wanda Ya Yi Nasara —Orji Kalu
  • Yau Litinin APC Za Ta Fara Tantance Masu Neman Takarar Shugaban Ƙasa

A tuhume-tuhume 17, Okorocha ana zarginsa da karkatar da N2.9bn daga asusun gwamnatin jihar Imo da na asusun hadaka na karamar hukumar jihar Imo da kamfanoni masu zaman kansu.

An bayyana cewa Okorocha da wani Anyim Inyerere ne suka yi amfani da kamfanoninsu masu zaman kansu tsakanin shekarar 2014 zuwa 2016 lokacin da yake rike da kujerar gwamnan jihar Imo.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Ko da yake ya musanta dukkan tuhume-tuhumen da ake yi masa, Okorocha, ya dauki manyan lauyoyin Nijeriya hudu da suka hada da Okey Amaechi, Solomon Umor, Ola Olanipekun da Kehinde Ogunwumiju, domin kare shi daga zargin da ake masa.

Jim kadan bayan karbar karar, lauyan EFCC, Gbolahan Latona, ya bukaci alkalin da a dage shari’ar domin ya samu damar hada shaidunsa da za su bayar da shaida yayin shari’a.

Ya shaida wa kotun cewa an shirya shaidu 15 da za su ba da shaida akan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar (APC) kuma akasarin shaidun ba sa hurumin kotun ne saboda kebantattun tuhume-tuhumen.

Lauyan Okorocha, Okey Amaechi, ya shaida wa kotun cewa ya shigar da bukatar naman belin wanda yake karewa, haka kuma ya taba yi wa EFCC.

Ya yi yunkurin yin gardama kan bukatar amma hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta nuna adawa da shi inda ta yi ikirarin cewa tana da niyyar shigar da kara kan bukatar belin.

Ko da yake, lauyan EFCC ya bukaci dage shari’ar zuwa ranar 1 ga watan Yuni, 2022 domin muhawara kan beli, Mai shari’a Ekwo ya yanke hukuncin cewa zai saurari bukatar belinsa a ranar 31 ga Mayu, ya kuma umurci EFCC da ta yi kokarin shigar da karar tata cikin lokaci.

Daga bisani mai shari’a Inyang Ekwo ya bayar da umarnin ci gaba da tsare Okorocha a hukumar EFCC har zuwa ranar 31 ga watan Mayu inda za a yi muhawara kan neman belinsa.

Okorocha
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
2023: Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar LP, Pat Utomi Ya Janyewa Peter Obi

2023: Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam'iyyar LP, Pat Utomi Ya Janyewa Peter Obi

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.