ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Oluremi Tinubu Ta Raba Naira Miliyan 50 Ga Dattawa 250 A Bauchi

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
5 days ago
Tinubu

A ƙalla dattawa 250 ne a jihar Bauchi suka amfana da tallafin Naira miliyan 50 a ƙarƙashin shirin tallafa wa dattawa na gidauniyar matar shugaban ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu ‘Renewed Hope Initiative Elderly Support Scheme’ (RHIESS).

 

Dattawan waɗanda kowanne ya amshi kyautar N200,000 lakadan a yayin ƙaddamar da shirin tallafa wa dattawa karo na uku da ya gudana a ranar Talata a filin wasanni na Dr. Rilwanu Sulaiman Adamu Square, da ke gidan gwamnatin jihar Bauchi, tallafin ya gudana ne a ƙarƙashin shirin gidauniyar na kyautata jin daɗi da walwalar jama’a.

ADVERTISEMENT
  • Shugaba Xi Ya Saurari Rahoton Aiki Daga Kantoman Yankin Musamman Na Hong Kong
  • Sin Ta Dauki Matakan Kakkaba Takunkumi Kan Tsohon Shugaban Rukunin Tsaron Kasar Japan

Da ta ke jawabi yayin miƙa kuɗaɗen ga waɗanda suka samu cin gajiya, Ko’odinetan gidauniyar RHI a Arewa Maso Gabas kuma matar gwamnan jihar Bauchi Dr. Aisha Bala Mohammed, ta nanata aniyar Gwamnatin tarayya na ci gaba da kyautata jin daɗi da walwalar dattawan mutane a faɗin ƙasar nan.

 

LABARAI MASU NASABA

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

A cewarta daga cikin Dattawan da suka amfana da tallafin a Bauchi an haɗa har da tsofaffin sojoji da ‘yansanda, tana mai cewa an yi hakan ne domin agaza musu da nema musu yadda rayuwa za ta ɗan yi musu sauƙi a matsayinsu na dattijai.

 

Ta ce a kowace jiha daga cikin jihohi 37 ciki har da FCT an zaɓi mutum 250 da za su amfana da wannan tallafin.

 

Da ta ke samun wakilcin matar mataimakin gwamnan jihar Bauchi, Hajiya Asma’u Muhammad Jatau, ta ce, taken tallafin shi ne ‘samar da farin ciki a zukatan dattawa,’ da aka yi da nufin kyautata musu rayuwa da mutuntasu.

 

A’isha Bala ta kuma yaba wa shugaban gidauniyar RHI, wato Sanata Oluremi Tinubu, bisa ƙoƙarinta na tallafa wa mutane musamman marasa ƙarfi a cikin al’umma.

 

Wasu da suka ci gajiyar tallafin sun gode wa matar shugaban ƙasa bisa kyautar, inda suka nuna cewa kuɗin zai rage musu raɗadin rayuwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa
Labarai

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli
Labarai

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Next Post
Wakilin Sin Ya Sake Gargadin Japan Da Ta Janye Kalamanta Na Kuskure

Wakilin Sin Ya Sake Gargadin Japan Da Ta Janye Kalamanta Na Kuskure

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.