• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ce Kaɗai Mai Karsashin Lashe Zaɓe – Atiku

by Sulaiman
3 years ago
PDP

Ɗan takarar zaɓen shugaban ƙasa na PDP a 2023, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa jam’iyyar sa kaɗai ce mai wani karsashin lashe zaɓe a yanzu.

Ya ce APC, jam’iyyar da ta kassara ƙasar nan har ta kusa durƙusar da ita, za ta ɓace, a neme ta a rasa bayan zaɓen 2023.

  • “Mun Yi Allah-Wadai Da Kai Wa Ayarin Atiku Hari A Jihar Borno” —Dattawan Arewa

Atiku ya yi wannan tsinkayen lokacin da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen sa ya ƙaddamar da Kwamitin Matasa na Yaƙin Neman Zaɓen PD (PDP-NYCN), ranar Alhamis, a Abuja.

“Maganar gaskiya, PDP kaɗai ce jam’iyya a Nijeriya. APC wani gungu ne kawai, kuma za mu yi nasarar korar su a ranar zaɓe. Mutuwa murus jam”iyyar za ta yi idan mu ka kore su daga kan mulki,” haka ya shaida wa matasa a wurin ƙaddamarwar.

“PDP za ta bai wa ɗimbin matasa dama a ƙasar nan, ba tare da yin la’akari ko nuna bambancin gida, arziki ko talaucin iyayen kowane matashi ba. Ko ɗan talaka ko ɗan wanene kai, PDP za ta taimake ka har ka cimma kyakkyawan ƙudirin ka a rayuwa.

LABARAI MASU NASABA

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

“Kai ko da Atiku ya kammala wa’adin sa ya sauka, to wani Atiku ɗin zai hau,” haka tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa daga 1999 zuwa 2007 ya jaddada.

Daga nan kuma ya hori PDP-NYCN su shiga ko’ina a faɗin ƙasar nan su wayar da kan matasa kafin zaɓe.

“Ku je ku ba su tabbaci, ku ƙarfafa masu guiwa da zukata. Ku nuna masu cewa duk matsalar da APC ta jefa ƙasar nan, har yanzu ana fatan maida ta kan turbar bunƙasa. Ku ɗauki wannan aiki da gaske, ku jajirce. Shi ne damar da za ku samu nan gaba, kuma shi ne damar iyalin ku da ƙasar ku.

“Saboda haka ina umartar ku da yin aiki tuƙuru domin ku ceto ƙasar nan, ta hanyar haɗa kan dukkan ‘yan Nijeriya, musamman musamman magoya bayan PDP.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
Siyasa

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
PDP
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Next Post
ASUU: Ndume Ya Bukaci A Zabtare Albashin ‘Yan Majalisa Kashi 50 Cikin 100 A Biya Malaman Jami’a

ASUU: Ndume Ya Bukaci A Zabtare Albashin 'Yan Majalisa Kashi 50 Cikin 100 A Biya Malaman Jami'a

LABARAI MASU NASABA

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.