• English
  • Business News
Monday, September 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Lashe Zabukan Cike Gurbi, Tsohon Kakakin Majalisar Bauchi Ya Dawo Majalisa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
PDP Ta Lashe Zabukan Cike Gurbi, Tsohon Kakakin Majalisar Bauchi Ya Dawo Majalisa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Kakakin Majalisar dokokin jihar Bauchi, Abubakar Y. Sulaiman, da tsohon mataimakinsa Umaru Dahiru Jamilu (PDP) sun sake komawa Majalisar dokokin jihar biyo bayan nasarar da suka samu a zaben cike gurbi da ya gudana a ranar Asabar. 

Abubakar ya samu nasara ne kan babban abokin karawarsa na jam’iyyar APC, Khalid Abdulmalik.

  • Zaɓen Cike-gurbi: NNPP Ta Yi Nasarar Lashe Zaɓen Kujeru Biyu Na Majalisar Jiha A Kano
  • Minista Idris Ya Ƙaddamar Da Ƙungiyar Kakakin Labarai 

Da yake sanar da sakamakon zaben, baturen zaben cike gurbin dan Majalisar Ningi, Farfesa Ahmad Abdulhameed ya ce Abubakar Y Sulaiman na PDP ya samu nasara ne da kuri’u 11,785 yayin da abokin nemansa na APC Khalid ya samu kuri’u 10,339.

Kazalika, a mazabar cikin garin Bauchi, Hon. Umaru Dahiru Jamilu na PDP shi ne ya lashe zaben cike gurbin, inda ya samu nasarar kayar da Kwamared Aliyu Ilale na jam’iyyar APC.

Baturen zaben mazabar Bauchi cikin gari, Farfesa Isma’ila Y Shehu ya ce, Umaru Dahiru Jamilu (PDP) ya lashe zaben ne da kuri’u 45,240 yayin da Abdullahi Aliyu (APC) ya samu kuri’u. 41,266.

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Bindiga Sun Kashe Dagacin Ogbayo Da Jami’an Ƴan Sa-Kai 11 A Kwara

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 14 A Borno Da Adamawa, Sun Ƙwato Makamai

Umaru Dahiru dai shi ne mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Bauchi kafin kotun daukaka kara ta soke nasarar da ya samu. Da wannan matakin zai sake komawa majalisa a matsayin mamba.

Haka zancen yake a mazabar wajen garin Bauchi wato Zungur/Galambi inda baturen zaben Farfesa Adamu Samaila na jami’ar ATBU ya shelanta Hon. Yusuf Ahmed na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben mazabar da kuri’u 2,233, hakan ya ba shi nasarar kayar da abokin nemansa Ibrahim Isa Yuguda na jam’iyyar APC da ya tashi da kuri’u 1,928.

Bugu da kari, kujerar dan majalisar Madada/Chinade kuwa, Baturen zaben mazabar, Farfesa Ahmed Abdulkadir ya ayyana Ala Nasiru Ahmed na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben da kuri’u 13,920 da ya mangare babban abokin nemansa na APC Dantala Ali mai samun kuri’u 9,710.

Jam’iyyar PDP da ke mulki a jihar ta Bauchi ta lashe dukkanin kujerun ‘yan majalisun da aka gudanar a zaben cike gurbi a mazabar Zungur/Galambi, Ningi, da Madara/Chinade.

Sake zaben na zuwa ne bayan da kotun daukaka kara ta soke nasarar da ‘yan majalisun hudu suka samu a zaben ranar 18 ga watan Maris na 2023. Bayan hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben mazabun, kotun daukaka kara ta umarci INEC ta sake gudanar da zabe a rumfuna 42 da suke gundumomin zabe 16 a cikin kananan hukumomi uku na Ningi, Bauchi da Katagum bayan kalubalantar nasarar su da abokan hamayyarsu suka yi.

Sai dai bayan saken zaben dukkanin wadanda aka yi jayayya a kan kujerun su sun sake dawowa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hukuncin Kotun kolisiyasar NijeriyaZabukan cike gurbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Ƙarshen Ƙalubalen Rashin Wutar Lantarki A Jere

Next Post

Zabukan Cike Gurbi: PDP Ta Lashe Kujera 2, APC 1 A Sakkwato

Related

Ƴan Bindiga Sun Kashe Dagacin Ogbayo Da Jami’an Ƴan Sa-Kai 11 A Kwara
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Dagacin Ogbayo Da Jami’an Ƴan Sa-Kai 11 A Kwara

8 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 14 A Borno Da Adamawa, Sun Ƙwato Makamai
Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 14 A Borno Da Adamawa, Sun Ƙwato Makamai

10 hours ago
Bayan Taron UNGA 80, Shettima Ya Nufi Jamus Don Tattaunawa Da Bankin Deutsche
Manyan Labarai

Bayan Taron UNGA 80, Shettima Ya Nufi Jamus Don Tattaunawa Da Bankin Deutsche

12 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Ceto Fasinjoji 8 Da Aka Sace A Kogi
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Ceto Fasinjoji 8 Da Aka Sace A Kogi

14 hours ago
Harin Bam: Gwamna Uba Sani Ya Kaddamar Da Sake Ginin Garin Tudun Biri 
Labarai

Gwamnatin Kaduna Za Ta Horas Da Ɗalibai 32,000 Sana’oin Hannu A Duk Shekara – Maiyaki

16 hours ago
Shari’a: Ganduje Ya Ki Na’am Da Tayin Jakadanci A Kasashen Afirka 
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Samu Kuɗaɗe A Cikin Wata 6 Fiye Da Yadda Na Samu A Cikin Shekaru 8 – Ganduje 

17 hours ago
Next Post
Zabukan Cike Gurbi: PDP Ta Lashe Kujera 2, APC 1 A Sakkwato

Zabukan Cike Gurbi: PDP Ta Lashe Kujera 2, APC 1 A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Za A Gudanar Da Bikin Ajiye Furanni Don Jinjinawa Jarumai A Ranar 30 Ga Satumba

Za A Gudanar Da Bikin Ajiye Furanni Don Jinjinawa Jarumai A Ranar 30 Ga Satumba

September 28, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Dagacin Ogbayo Da Jami’an Ƴan Sa-Kai 11 A Kwara

Ƴan Bindiga Sun Kashe Dagacin Ogbayo Da Jami’an Ƴan Sa-Kai 11 A Kwara

September 28, 2025
Ana Hasashen Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Yayin Hutun Bikin Tsakiyar Kaka Na Sin Zai Kai Biliyan 2.36

Ana Hasashen Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Yayin Hutun Bikin Tsakiyar Kaka Na Sin Zai Kai Biliyan 2.36

September 28, 2025
Firimiyar Nijeriya: Barau FC Ta Samu Nasarar Farko A Tarihinta

Firimiyar Nijeriya: Barau FC Ta Samu Nasarar Farko A Tarihinta

September 28, 2025
Kwararrun Afirka Sun Jinjinawa Hadin Gwiwar Kirkire-Kirkire Tsakanin Kasashen Nahiyar Da Sin

Kwararrun Afirka Sun Jinjinawa Hadin Gwiwar Kirkire-Kirkire Tsakanin Kasashen Nahiyar Da Sin

September 28, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 14 A Borno Da Adamawa, Sun Ƙwato Makamai

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 14 A Borno Da Adamawa, Sun Ƙwato Makamai

September 28, 2025
CMG Ya Yi Ayyukan Hadin Gwiwa Da Bangarori Daban Daban Na Macao

CMG Ya Yi Ayyukan Hadin Gwiwa Da Bangarori Daban Daban Na Macao

September 28, 2025
Bayan Taron UNGA 80, Shettima Ya Nufi Jamus Don Tattaunawa Da Bankin Deutsche

Bayan Taron UNGA 80, Shettima Ya Nufi Jamus Don Tattaunawa Da Bankin Deutsche

September 28, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Makarantun Horar Da ‘Yan Jam’iyya Da Su Kara Azamar Kyankyashe Hazikai Da Gabatar Da Shawarwari Ga JKS

Xi Ya Yi Kira Ga Makarantun Horar Da ‘Yan Jam’iyya Da Su Kara Azamar Kyankyashe Hazikai Da Gabatar Da Shawarwari Ga JKS

September 28, 2025
Gwamna Makinde Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Nijeriya da Naira Miliyan 22

Gwamna Makinde Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Nijeriya da Naira Miliyan 22

September 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.