• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Lashe Zabukan Cike Gurbi, Tsohon Kakakin Majalisar Bauchi Ya Dawo Majalisa

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
PDP Ta Lashe Zabukan Cike Gurbi, Tsohon Kakakin Majalisar Bauchi Ya Dawo Majalisa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Kakakin Majalisar dokokin jihar Bauchi, Abubakar Y. Sulaiman, da tsohon mataimakinsa Umaru Dahiru Jamilu (PDP) sun sake komawa Majalisar dokokin jihar biyo bayan nasarar da suka samu a zaben cike gurbi da ya gudana a ranar Asabar. 

Abubakar ya samu nasara ne kan babban abokin karawarsa na jam’iyyar APC, Khalid Abdulmalik.

  • Zaɓen Cike-gurbi: NNPP Ta Yi Nasarar Lashe Zaɓen Kujeru Biyu Na Majalisar Jiha A Kano
  • Minista Idris Ya Ƙaddamar Da Ƙungiyar Kakakin Labarai 

Da yake sanar da sakamakon zaben, baturen zaben cike gurbin dan Majalisar Ningi, Farfesa Ahmad Abdulhameed ya ce Abubakar Y Sulaiman na PDP ya samu nasara ne da kuri’u 11,785 yayin da abokin nemansa na APC Khalid ya samu kuri’u 10,339.

Kazalika, a mazabar cikin garin Bauchi, Hon. Umaru Dahiru Jamilu na PDP shi ne ya lashe zaben cike gurbin, inda ya samu nasarar kayar da Kwamared Aliyu Ilale na jam’iyyar APC.

Baturen zaben mazabar Bauchi cikin gari, Farfesa Isma’ila Y Shehu ya ce, Umaru Dahiru Jamilu (PDP) ya lashe zaben ne da kuri’u 45,240 yayin da Abdullahi Aliyu (APC) ya samu kuri’u. 41,266.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Umaru Dahiru dai shi ne mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Bauchi kafin kotun daukaka kara ta soke nasarar da ya samu. Da wannan matakin zai sake komawa majalisa a matsayin mamba.

Haka zancen yake a mazabar wajen garin Bauchi wato Zungur/Galambi inda baturen zaben Farfesa Adamu Samaila na jami’ar ATBU ya shelanta Hon. Yusuf Ahmed na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben mazabar da kuri’u 2,233, hakan ya ba shi nasarar kayar da abokin nemansa Ibrahim Isa Yuguda na jam’iyyar APC da ya tashi da kuri’u 1,928.

Bugu da kari, kujerar dan majalisar Madada/Chinade kuwa, Baturen zaben mazabar, Farfesa Ahmed Abdulkadir ya ayyana Ala Nasiru Ahmed na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben da kuri’u 13,920 da ya mangare babban abokin nemansa na APC Dantala Ali mai samun kuri’u 9,710.

Jam’iyyar PDP da ke mulki a jihar ta Bauchi ta lashe dukkanin kujerun ‘yan majalisun da aka gudanar a zaben cike gurbi a mazabar Zungur/Galambi, Ningi, da Madara/Chinade.

Sake zaben na zuwa ne bayan da kotun daukaka kara ta soke nasarar da ‘yan majalisun hudu suka samu a zaben ranar 18 ga watan Maris na 2023. Bayan hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben mazabun, kotun daukaka kara ta umarci INEC ta sake gudanar da zabe a rumfuna 42 da suke gundumomin zabe 16 a cikin kananan hukumomi uku na Ningi, Bauchi da Katagum bayan kalubalantar nasarar su da abokan hamayyarsu suka yi.

Sai dai bayan saken zaben dukkanin wadanda aka yi jayayya a kan kujerun su sun sake dawowa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hukuncin Kotun kolisiyasar NijeriyaZabukan cike gurbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Ƙarshen Ƙalubalen Rashin Wutar Lantarki A Jere

Next Post

Zabukan Cike Gurbi: PDP Ta Lashe Kujera 2, APC 1 A Sakkwato

Related

Sanusi
Manyan Labarai

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

3 hours ago
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 
Labarai

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

6 hours ago
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

7 hours ago
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus
Manyan Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

10 hours ago
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

13 hours ago
Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet
Manyan Labarai

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

14 hours ago
Next Post
Zabukan Cike Gurbi: PDP Ta Lashe Kujera 2, APC 1 A Sakkwato

Zabukan Cike Gurbi: PDP Ta Lashe Kujera 2, APC 1 A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

June 3, 2025
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

June 3, 2025
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

June 3, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.