• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Mayar Da Martani Mai Zafi Ga APC Kan Neman Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Zamfara

by Leadership Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
PDP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’iyyar PDP a Jihar Zamfara, ta bayyana kiran da jam’iyyar APC ƙarƙashin jagorancin tsofaffin Gwamnanonin jihar, Bello Matawalle da Sanata Abdulaziz Yari suka yi na ayyana dokar ta-baci a jihar a matsayin “hassada” da ci gaban da aka samu a ƙarƙashin jagorancin Gwamna Dauda Lawal.

 

A wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labaran Jami’iyyar PDP na Zamfara, Halliru Andi ya fitar a ranar, 22 ga Satumba, 2024, ta ce, “Gwamnatin PDP ta mayar da hankali ne wajen gyara kura-kuran da gwamnatocin baya suka tafka na tsawon shekaru a jihar.

  • Zamfara Ta Bayar Da Gudunmawar Miliyan 100 Ga Waɗanda Ambaliya Ta Shafa a Borno 
  • Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Mutuwar Mutane 40 A Hatsarin Kwale-kwale

“Kiran a kafa dokar ta-baci ba shi da tushe balle makama kuma rashin mutunta al’ummar jihar Zamfara ne. Jam’iyyar APC ta yi biris da abubuwan da suka shafi tsohon Gwamna Bello Matawalle, wanda rashin sanin makamar aikin sa ne ya ƙara dagula harkar tsaro a jihar.

 

Labarai Masu Nasaba

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

“Rashin tabbatar da tsaro da gwamnatinsa ta yi ya samo asali ne yayin da ta riƙa ƙirƙirar samar wa ’yan ta’adda da wurin zama da sunan “sulhu”, ciki har da bayar da motocin Hilux da kuma tukuicin kuɗi ga ’yan bindigar, tare da ba su damar shiga gidan gwamnati kai tsaye. Wannan ya sa al’ummar Zamfara suka gamu da mugun nufi na wannan sakaci, inda ’yan bindiga ke afka wa al’umma sannan su koma su fake a bayan masu mulki.

 

“Ikirarin rashin gaskiya na cewa, Gwamna Dauda Lawal na yin zagon ƙasa a yaƙin da ake yi da ’yan bindiga a Jihar Zamfara, wani yunƙuri ne na siyasa domin kawo cikas ga ƙoƙarin da muke yi na magance matsalar rashin tsaro a jihar,” in ji sanarwar.

 

Ta ƙara da cewa, “Gwamna Lawal shi ne na farko a tarihin jiharmu da ya ba da fifiko kan harkokin tsaro tare da jajircewa na gaskiya, sabanin yadda gwamnatocin APC da suka shuɗe suka yi.

 

“Ba kamar jam’iyyar APC da ta siyasantar da matsalar rashin tsaro ba, gwamnatin PDP ta himmatu wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Zamfara. Nasarorin da muka samu a kan ‘yan bindiga sun samo asali ne daga jajircewar Gwamna Lawal, na ƙin yin sulhu da masu laifi. Wannan matsaya mai ƙarfi ta kafa tabbataccen alƙibla a yaƙinmu da ‘yan ta’addan.

 

“Gwamnatin PDP ƙarƙashin jagorancin Gwamna Dauda Lawal ta ɗauki muhimman matakai da suka haɗa da kafa Rundunar Tsaron Kare Al’umma ‘Askarawan Zamfara’ (CPG) da kuma samar da asusun kula da tsaro domin tallafawa jami’an tsaro. Makonni kaɗan da suka gabata Gwamna Lawal ya raba motoci domin inganta ayyukan hukumomin tsaro, inda ya nuna jajircewarsa kan wannan lamari mai matuƙar muhimmanci,” in ji sanarwa.

 

Sanarwar ta ce, “Zargin da APC ke yi, farfaganda ce kawai. Ko kaɗan tsohon Gwamna Matawalle bai bayyana aniyar haɗa kai da Gwamna Lawal wajen magance matsalar rashin tsaro ba. Bugu da ƙari, Matawalle, wanda yanzu shi ne ƙaramin ministan tsaro, ya nuna rashin ƙwarewa da kuma rashin tausayawa ga al’ummar Zamfara. Tattaunawar da ya yi a asirce da ’yan bindiga, ba tare da sanin Gwamna Lawal ba, kai tsaye ya ruguza tsayuwar gwamnatin da ta yi hannun riga da batun yin sulhu da ‘yan bindiga. Bayan rashin nasarar wannan tattaunawar, ya yi ikirarin ƙarya cewa Gwamna Lawal ya amince da Naira biliyan 1.3 a cikin wata takarda da aka ƙirƙira domin sulhuntawa da ’yan ta’adda, magana mara tushe.”

 

Ta ce, “Muna kira ga shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya kori Bello Matawalle daga muƙaminsa na ƙaramin ministan tsaro. Rashin amincinsa da rashin cancantar wannan matsayi ya bayyana ƙarara a cikin ayyukan da ya yi a baya, wanda ba kawai ya lalata yaƙin da ake yi da ‘yan binidiga a halin yanzu ba ne, har ma kawo haɗari ga lafiyar ‘yan ƙasarmu. Ya zama wajibi gwamnatin tarayya ta binciki matakan da Matawalle ya ɗauka, musamman alaƙar sa da shugabannin ’yan bindiga, waɗanda ke zama cikas ga shugabanci nagari.”

 

“A ƙarshe muna kira ga jam’iyyar APC da ta mayar da hankali kan al’amuran da suka shafi jihar Zamfara, maimakon yin tuhume-tuhume da karkatar da hankalin al’umma. Gwamna Dauda Lawal dai ya tsaya tsayin daka kan ƙudirinsa na kawo sauyi a jihar, kuma ba zai sa ya yi ƙasa a gwiwa ba da ikirarin da ‘yan adawa ke yi. Al’ummar Zamfara na buƙatar zaman lafiya, kuma wannan gwamnati ta himmatu wajen ganin ta cika wannan alƙawarin da ta ɗauka,” in ji sanarwar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: SiyasaTa'addancin 'yan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Ba Da Belin Mawaki P Diddy Mai Safarar Mata

Next Post

An Gudanar Da Bikin Da Ya Shafi Makamashi Na Nan Gaba A Birnin New York

Related

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

45 minutes ago
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata
Labarai

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

2 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

5 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

7 hours ago
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa
Labarai

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

8 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

9 hours ago
Next Post
An Gudanar Da Bikin Da Ya Shafi Makamashi Na Nan Gaba A Birnin New York

An Gudanar Da Bikin Da Ya Shafi Makamashi Na Nan Gaba A Birnin New York

LABARAI MASU NASABA

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.