ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zamfara Ta Bayar Da Gudunmawar Miliyan 100 Ga Waɗanda Ambaliya Ta Shafa a Borno 

by Abubakar Sulaiman
2 years ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jajanta wa gwamnati da al’ummar Jihar Borno sakamakon mummunar ambaliyar ruwa da ta afku a Maiduguri.

A ranar Alhamis ɗin da ta gabata ne wata tawaga ƙarƙashin jagorancin Mallam Abubakar Nakwada, Sakataren Gwamnatin Jihar Zamfara, ta wakilci gwamnan a Maiduguri.

  • Hatsarin Kwalekwale A Zamfara: Asalin Abin Da Ya Faru Da Yadda Wasu Suka Tsira
  • Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Raya Daren Maulidin Bana Duk Da Mamakon Ruwan Sama

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa maƙasudin ziyarar ita ce jajanta wa Gwamnatin Borno da al’ummar jihar kan ambaliyar ruwa mai ratsa zuciya.

ADVERTISEMENT

Yayin da yake miƙa saƙon jaje na Gwamna Lawal a fadar gwamnatin jihar Borno, Mallam Abubakar Nakwada ya sanar da gudunmawar Naira Miliyan 100 da gwamnatin jihar Zamfara ta bayar a matsayin nuna goyon baya da tallafawa.

Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Ya ce, “A madadin jama’a da gwamnatin jihar Zamfara, ina rubutu domin nuna alhininmu game da mummunar ambaliyar ruwa da ta afku sakamakon ballewar ruwa daga madatsar ruwa ta Alu da ke Maiduguri.

“Muna matuƙar baƙin ciki da rahotannin da ke cewa sama da mutum miliyan ɗaya ne suka rasa muhallansu sakamakon wannan ibtila’i.

“Lamarin wannan ibtila’i yana ratsa zuciya. Al’ummar jihar Zamfara – waɗanda suka fuskanci irin wannan ibtila’i, duk da cewa bai kai na Borno ba – suna yi wa ‘yan uwansu maza da mata a yankunan abin ya shafa addu’ar ‘Allah Ya mayar da alkhairi, Ya kuma kiyaye faruwar hakan a nan gaba’, yayin da suke cikin wannan mawuyacin hali. Muna roƙon Allah Ta’ala ya jiƙan waɗanda suka rasa rayukansu, ya kuma mayar wa waɗanda suka rasa dukiyoyinsu da mafificin alkhairi.

“A matsayin nuna goyon baya da tallafawa, gwamnatin jihar Zamfara na bayar da gudunmawar zunzurutun kuɗi Naira Miliyan 100,000 domin gudanar da ayyukan agaji da kuma taimaka wa al’ummomin da abin ya shafa a Maiduguri.

“Muna roƙon Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya ci gaba da taimakon waɗanda abin ya shafa, ya ba su ƙarfin gwiwa da juriya wajen sake gina rayuwarsu.

Zamfara
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu
  • Abubakar Sulaiman
    Enekweci Ne Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya A Wasannin Commonwealth Na Bana
  • Abubakar Sulaiman
    Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi
  • Abubakar Sulaiman
    Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje
Labarai

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
Labarai

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Next Post
Fasahar Sin Ta Kara Habaka Sha’anin Zirga-zirgar Ababen Hawa Mara Gurbata Muhalli A Afrika

Fasahar Sin Ta Kara Habaka Sha’anin Zirga-zirgar Ababen Hawa Mara Gurbata Muhalli A Afrika

LABARAI MASU NASABA

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.