• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Yi Satar Amsa Daga Manufofin Buhari – Tinubu

by Leadership Hausa
3 years ago
in Siyasa
0
PDP Ta Yi Satar Amsa Daga Manufofin Buhari – Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A halin da ake ciki kuma, Dan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu ya zargi PDP da dan takarar shugaban kasanta, Atiku Abubakar waje satar amsa daga manufofin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari.

Tinubu ya zargi Atiku da satar manufofin Buhari guda biyar wanda ya saka su a cikin shafukan yakin neman zabensa guda 74. Dan takarar shugaban kasa na APC ya ce jam’iyyar PDP ba ta da kwarewawajen yin sahihin adawa.

  • Kasar Sin Mai Wadata Za Ta Kara Samar Da Damammaki Ga Duniya
  • Neymar Ya Zura Kwallaye 200 A Kungiyoyi Uku

Babban mai magana da yawun dan takarar wanda shi ne daraktan hulda da jama’a na kwamitin yakin neman zabe, Festus Keyamo (SAN), shi ya bayyana hakan lokacin da yake mayar da martani kan ikirarin daraktan yada labarai na yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na PDP,

Dele Momodu kan fejina 80 da Tinubu ya bayyana a matsayin manufofinsa a Abuja ranar Asabar a filin wasa na MKO Abiola.

Da yake mayar da martanin, Keyamo wanda ya kasance tsohon ministan samar da ayyuka yi ya ce tawagar kamfen din Atiku marasa amfani ne.

Labarai Masu Nasaba

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

Ya ce ya yi tsammanin cewa Momodu zai yi cikakken bayani a tsakanin kundin mai dauke da shafuka 93 da Tinubu ya kaddamar da filin wasa na MKO Abiola.

Ya ce Atiku ya sace manufofi guda biyar na Buhari wanda ya cike a kundin yakin neman zabensa.

Ya ce daga cikin manufofin akwai fitar da miliyoyin mutane daga kangin talauci da sake farfado da wutar lantarki wajen bunkasa tattalin arziki, wanda kamata ya yi ya kirkiri nasa sababbin manufofin ba wai ya tsaya satar na Shugaba Buhari ba.

Keyamo ya ci gaba da bayyana cewa Momodu bai da abun da zai iya sukar Tinubu, domin ya yi kokarin kawo  nasa manufofin ba tare da ya sata dagawurin wani ba.

Zan Fallasa Badakalar APC – Atiku

Dan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya bayyana cewa zai fallasa dukkan badakalar da jam’iyyar APC ta yi lokacin da take rike da madafun iko bayan ya samu nasarar zama shugaban kasa.

Atiku ya bayyana haka ne lokacin da yake yi wa magoya bayansa jawabi a ranar Lahadin da ta gabata, ya siffanta babban zaben 2023 a matsayin raba gardama game da kwazon APC.

Ya kara da cewa jam’iyyar APC da kuma dan takarar shugaban kasarta, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu suna so su ci gaba da mulki duk da irin zagawa da suka yi, amma jam’iyyar PDP ba zata taba barin su ba.

Ya ce, “Lokacin da muka ziyarci Benin na bayyana manufofi na kararawajen gudunar da ayyuka da zai hade kanmu da ceto kasarmu Nijeriya.

“Shiri ne wanda ya kunshi dogon zango mai matukar kalubale a gare mu a halin yanzu, wanda dalilin da ya saya kin neman zabena ya karkata wajen tallafa su ga ‘yan Nijeriya kenan.

“A bangarena da kuma duk wanda yake a cikin jam’iyyar PDP, babban zaben 2023 shi ne zakaran gwajin dafi da zai auna kwazon APC.

“Jam’iyya mai mulki na kokarin gudu daga rashin gwazon su wanda hasali ma suna mayar da hankali akan abubuwan da ba su ta’allaka da zaben ba. Amma mu ba za mu taba basu dama ba. Sai mun bankado duk irin tsula tsiyar da suka tabka mun bayyanawa ‘yan Nijeriya.

“Ko da yake hakan ba zai gamsar ba. Abin da ya fi muhimmanci shi ne, karmu sake maimaita kuskuren da muka yi a baya.

“Wannan ya sa muka hadu domin mu bayyana muku manufofin kowacce jam’iyyar siyasa domin yanke hukuncin da ya dace lokacin zabe.”

Atiku jaddada cewa a matsayinsa na dan takarar shugaban kasa a karkashin inuwar jam’iyyar PDP, zai mayar da hankali ga dukkan matsaloli da suka addabi kasar nan.

Sulhu Tsakanin Atiku Da Wike Ya Sha Ruwa

Daga karshe dai, sulhu a tsakanin gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Ezenwo Wike da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya sha ruwa.

Wike ya bayyana cewa ba zai yi wa jam’iyyar PDP yakin neman zabe ba saboda ba a tuntube shi ba lokacin da aka dauki mambobin kamfen a cikin jiharsa.

Ya kara da cewa hotonan Atiku da na shugaban jam’iyyar PDP, Sanata Iyorchia Ayu sun yi batan dabo a cikin jiharsa saboda ba su san yayi yakin neman zabe a mataki na tarayya a jam’iyyar.

Wike ya bayyana hakan ne a lokacin kaddamar da kwamitin kamfen din jam’iyyar PDP a Jihar Ribas wanda ya gudana a garin Fatakwal.

Ya ce dan takarar shugaban kasa a jam’iyyary a zabi makiya Jihar Ribas a cikin kwamitin yakin neman zabensa na 2023.

Gwamnan ya ce, “Wasu mutane suna tambaya na kan dalilan da suka sa ba a ganin hotunan dan takarar shugaban kasa da kuma na shugaban jam’iyyar. Na ce musu me ye suke magana a kai? Dan takarar shugaban kasa ya shiga jihata ya dauko mambobin kwamitin yakin neman zabensa ba tare da gudummuwar gwamnan jihar ba.

“Dan takarar shugaban kasa ya shiga Jihar Ribas ya dauko wadanda yake bukata ba tare da bayar da gudummuwar gwamna ba. Sun ce basa bukata na a yakin neman zabensu, kuma hakan na nuna cewa ba sabukatar mutanen Jihar Ribas ne a cikin kwamitin kamfen dinsu.”

Wike ya ce shi da sauran ‘ya’yan jam’iyyar a jihar za su yi kamfen ne kadai ga dan takarar gwamna da na sanata da sauran wasu mukamai, amma ban da na dan takarar shugaban kasa.

Ya ce, “Idan da suna bukatarmu a cikin yakin neman zabensu da sun tuntube mu. Idan yana tunanin muna da muhimmanci, to da ya zo wurinmu. Babu wanda ya isa ya jagoranci Jihar Ribas fiye da ni a matsayina na gwamnan jihar.”

Gwamnan ya kara da cewa kowacce karamar hukumar guda 23 da ke jihar tana da hanyoyin da take bi wajen hada mutanenta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCAtikuBuhariPDPTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Mahangar ECOWAS Kan Zaben Nijeriya

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa
Labarai

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

1 day ago
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027
Siyasa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

2 days ago
NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC
Siyasa

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

2 days ago
Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu
Siyasa

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

3 days ago
Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP
Siyasa

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

4 days ago
Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye
Siyasa

Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye

7 days ago
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.