• Leadership Hausa
Tuesday, December 5, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Yi Satar Amsa Daga Manufofin Buhari – Tinubu

by Leadership Hausa
1 year ago
in Siyasa
0
PDP Ta Yi Satar Amsa Daga Manufofin Buhari – Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A halin da ake ciki kuma, Dan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu ya zargi PDP da dan takarar shugaban kasanta, Atiku Abubakar waje satar amsa daga manufofin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari.

Tinubu ya zargi Atiku da satar manufofin Buhari guda biyar wanda ya saka su a cikin shafukan yakin neman zabensa guda 74. Dan takarar shugaban kasa na APC ya ce jam’iyyar PDP ba ta da kwarewawajen yin sahihin adawa.

  • Kasar Sin Mai Wadata Za Ta Kara Samar Da Damammaki Ga Duniya
  • Neymar Ya Zura Kwallaye 200 A Kungiyoyi Uku

Babban mai magana da yawun dan takarar wanda shi ne daraktan hulda da jama’a na kwamitin yakin neman zabe, Festus Keyamo (SAN), shi ya bayyana hakan lokacin da yake mayar da martani kan ikirarin daraktan yada labarai na yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na PDP,

Dele Momodu kan fejina 80 da Tinubu ya bayyana a matsayin manufofinsa a Abuja ranar Asabar a filin wasa na MKO Abiola.

Da yake mayar da martanin, Keyamo wanda ya kasance tsohon ministan samar da ayyuka yi ya ce tawagar kamfen din Atiku marasa amfani ne.

Labarai Masu Nasaba

Ana Fargabar Sakamakon Hukuncin Zaben Gwamnan Sokoto Da Kotu Za Ta Yanke Yau Litinin

Gwamnan Jihar Filato Zai Garzaya Kotun Ƙoli Don Ƙalubalantar Hukuncin Soke Zaɓensa

Ya ce ya yi tsammanin cewa Momodu zai yi cikakken bayani a tsakanin kundin mai dauke da shafuka 93 da Tinubu ya kaddamar da filin wasa na MKO Abiola.

Ya ce Atiku ya sace manufofi guda biyar na Buhari wanda ya cike a kundin yakin neman zabensa.

Ya ce daga cikin manufofin akwai fitar da miliyoyin mutane daga kangin talauci da sake farfado da wutar lantarki wajen bunkasa tattalin arziki, wanda kamata ya yi ya kirkiri nasa sababbin manufofin ba wai ya tsaya satar na Shugaba Buhari ba.

Keyamo ya ci gaba da bayyana cewa Momodu bai da abun da zai iya sukar Tinubu, domin ya yi kokarin kawo  nasa manufofin ba tare da ya sata dagawurin wani ba.

Zan Fallasa Badakalar APC – Atiku

Dan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya bayyana cewa zai fallasa dukkan badakalar da jam’iyyar APC ta yi lokacin da take rike da madafun iko bayan ya samu nasarar zama shugaban kasa.

Atiku ya bayyana haka ne lokacin da yake yi wa magoya bayansa jawabi a ranar Lahadin da ta gabata, ya siffanta babban zaben 2023 a matsayin raba gardama game da kwazon APC.

Ya kara da cewa jam’iyyar APC da kuma dan takarar shugaban kasarta, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu suna so su ci gaba da mulki duk da irin zagawa da suka yi, amma jam’iyyar PDP ba zata taba barin su ba.

Ya ce, “Lokacin da muka ziyarci Benin na bayyana manufofi na kararawajen gudunar da ayyuka da zai hade kanmu da ceto kasarmu Nijeriya.

“Shiri ne wanda ya kunshi dogon zango mai matukar kalubale a gare mu a halin yanzu, wanda dalilin da ya saya kin neman zabena ya karkata wajen tallafa su ga ‘yan Nijeriya kenan.

“A bangarena da kuma duk wanda yake a cikin jam’iyyar PDP, babban zaben 2023 shi ne zakaran gwajin dafi da zai auna kwazon APC.

“Jam’iyya mai mulki na kokarin gudu daga rashin gwazon su wanda hasali ma suna mayar da hankali akan abubuwan da ba su ta’allaka da zaben ba. Amma mu ba za mu taba basu dama ba. Sai mun bankado duk irin tsula tsiyar da suka tabka mun bayyanawa ‘yan Nijeriya.

“Ko da yake hakan ba zai gamsar ba. Abin da ya fi muhimmanci shi ne, karmu sake maimaita kuskuren da muka yi a baya.

“Wannan ya sa muka hadu domin mu bayyana muku manufofin kowacce jam’iyyar siyasa domin yanke hukuncin da ya dace lokacin zabe.”

Atiku jaddada cewa a matsayinsa na dan takarar shugaban kasa a karkashin inuwar jam’iyyar PDP, zai mayar da hankali ga dukkan matsaloli da suka addabi kasar nan.

Sulhu Tsakanin Atiku Da Wike Ya Sha Ruwa

Daga karshe dai, sulhu a tsakanin gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Ezenwo Wike da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya sha ruwa.

Wike ya bayyana cewa ba zai yi wa jam’iyyar PDP yakin neman zabe ba saboda ba a tuntube shi ba lokacin da aka dauki mambobin kamfen a cikin jiharsa.

Ya kara da cewa hotonan Atiku da na shugaban jam’iyyar PDP, Sanata Iyorchia Ayu sun yi batan dabo a cikin jiharsa saboda ba su san yayi yakin neman zabe a mataki na tarayya a jam’iyyar.

Wike ya bayyana hakan ne a lokacin kaddamar da kwamitin kamfen din jam’iyyar PDP a Jihar Ribas wanda ya gudana a garin Fatakwal.

Ya ce dan takarar shugaban kasa a jam’iyyary a zabi makiya Jihar Ribas a cikin kwamitin yakin neman zabensa na 2023.

Gwamnan ya ce, “Wasu mutane suna tambaya na kan dalilan da suka sa ba a ganin hotunan dan takarar shugaban kasa da kuma na shugaban jam’iyyar. Na ce musu me ye suke magana a kai? Dan takarar shugaban kasa ya shiga jihata ya dauko mambobin kwamitin yakin neman zabensa ba tare da gudummuwar gwamnan jihar ba.

“Dan takarar shugaban kasa ya shiga Jihar Ribas ya dauko wadanda yake bukata ba tare da bayar da gudummuwar gwamna ba. Sun ce basa bukata na a yakin neman zabensu, kuma hakan na nuna cewa ba sabukatar mutanen Jihar Ribas ne a cikin kwamitin kamfen dinsu.”

Wike ya ce shi da sauran ‘ya’yan jam’iyyar a jihar za su yi kamfen ne kadai ga dan takarar gwamna da na sanata da sauran wasu mukamai, amma ban da na dan takarar shugaban kasa.

Ya ce, “Idan da suna bukatarmu a cikin yakin neman zabensu da sun tuntube mu. Idan yana tunanin muna da muhimmanci, to da ya zo wurinmu. Babu wanda ya isa ya jagoranci Jihar Ribas fiye da ni a matsayina na gwamnan jihar.”

Gwamnan ya kara da cewa kowacce karamar hukumar guda 23 da ke jihar tana da hanyoyin da take bi wajen hada mutanenta.

Tags: APCAtikuBuhariPDPTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Mahangar ECOWAS Kan Zaben Nijeriya

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Kotun Zaben Gwamnan Sokoto Ta Kori Karar PDP Ta Tabbatar Da Nasarar Zaben Aliyu
Da ɗumi-ɗuminsa

Ana Fargabar Sakamakon Hukuncin Zaben Gwamnan Sokoto Da Kotu Za Ta Yanke Yau Litinin

1 week ago
Gwamnan Jihar Filato Zai Garzaya Kotun Ƙoli Don Ƙalubalantar Hukuncin Soke Zaɓensa
Manyan Labarai

Gwamnan Jihar Filato Zai Garzaya Kotun Ƙoli Don Ƙalubalantar Hukuncin Soke Zaɓensa

2 weeks ago
Kotu Ta Kori Karar Abba K. Yusuf Ta Tabbatar Da Hukuncin Kotun Zabe Da Ya Tabbatar Da Gawuna
Manyan Labarai

Kotu Ta Kori Karar Abba K. Yusuf Ta Tabbatar Da Hukuncin Kotun Zabe Da Ya Tabbatar Da Gawuna

3 weeks ago
Jerin Sunayen Sabbin Ministocin Da Buhari Ya Aike Wa Majalisar Dattijai Ta Tantance Su
Siyasa

Buhari Ya Taya APC Murnar Nasarar Lashe Zaben Gwamnoni A Jihohin Imo Da Kogi

3 weeks ago
INEC Ta Ayyana Uzodimma Na APC A Matsayin Wanda Ya Lashe Zaben Gwamnan Imo
Manyan Labarai

INEC Ta Ayyana Uzodimma Na APC A Matsayin Wanda Ya Lashe Zaben Gwamnan Imo

3 weeks ago
Kotun Daukaka Karar Zaben Gwamnan Kano Za Ta Sanar Da Ranar Yanke Hukunci Kan Shari’ar
Manyan Labarai

Kotun Daukaka Karar Zaben Gwamnan Kano Za Ta Sanar Da Ranar Yanke Hukunci Kan Shari’ar

4 weeks ago
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Da Na Gaba Ake Gane Zurfin Ruwa

Da Na Gaba Ake Gane Zurfin Ruwa

December 4, 2023
An Rufe Taron Fahimtar Sin Na shekarar 2023

An Rufe Taron Fahimtar Sin Na shekarar 2023

December 4, 2023
Kotu Ta Umarci Dawo Da Motoci 50 Da Tsohon Gwamnan Zamfara Ya Kwashe

Kotu Ta Umarci Dawo Da Motoci 50 Da Tsohon Gwamnan Zamfara Ya Kwashe

December 4, 2023
Kasafin 2024 Ya Bada Fifiko Ne Wajen Jaddada Ajandar Saisaita Nijeriya – Minista

Kasafin 2024 Ya Bada Fifiko Ne Wajen Jaddada Ajandar Saisaita Nijeriya – Minista

December 4, 2023
Gwamnatin Birtaniya Na Damuwa Kan Yadda Ake Neman A Mayar Da Kayayyakin Tarihi Da Ta Mallaka

Gwamnatin Birtaniya Na Damuwa Kan Yadda Ake Neman A Mayar Da Kayayyakin Tarihi Da Ta Mallaka

December 4, 2023
Babban Edita Dan Kasar Ghana: A Bayyana Yadda Sin Da Afirka Suke Hadin Gwiwa Da Juna

Babban Edita Dan Kasar Ghana: A Bayyana Yadda Sin Da Afirka Suke Hadin Gwiwa Da Juna

December 4, 2023
Sojojin Nijeriya Sun Dauki Alhakin Kai Harin Bam Cikin Kuskure A Wurin Taron Mauludi A Kaduna

Sojojin Nijeriya Sun Dauki Alhakin Kai Harin Bam Cikin Kuskure A Wurin Taron Mauludi A Kaduna

December 4, 2023
Jami’ar EDF: Matakan Lardin Guangdong Na Sin Kan Magance Sauyin Yanayi Abin Koyi Ne

Jami’ar EDF: Matakan Lardin Guangdong Na Sin Kan Magance Sauyin Yanayi Abin Koyi Ne

December 4, 2023
Yadda Likitocin Nijeriya 1,616 Suka Koma Aiki Zuwa Kasar Birtaniya 

Yadda Likitocin Nijeriya 1,616 Suka Koma Aiki Zuwa Kasar Birtaniya 

December 4, 2023
Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Kasa Da Kasa Na Congdu Na 2023

Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Kasa Da Kasa Na Congdu Na 2023

December 4, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.