ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 23, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Yi Satar Amsa Daga Manufofin Buhari – Tinubu

by Leadership Hausa
4 years ago
PDP

A halin da ake ciki kuma, Dan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu ya zargi PDP da dan takarar shugaban kasanta, Atiku Abubakar waje satar amsa daga manufofin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari.

Tinubu ya zargi Atiku da satar manufofin Buhari guda biyar wanda ya saka su a cikin shafukan yakin neman zabensa guda 74. Dan takarar shugaban kasa na APC ya ce jam’iyyar PDP ba ta da kwarewawajen yin sahihin adawa.

  • Kasar Sin Mai Wadata Za Ta Kara Samar Da Damammaki Ga Duniya
  • Neymar Ya Zura Kwallaye 200 A Kungiyoyi Uku

Babban mai magana da yawun dan takarar wanda shi ne daraktan hulda da jama’a na kwamitin yakin neman zabe, Festus Keyamo (SAN), shi ya bayyana hakan lokacin da yake mayar da martani kan ikirarin daraktan yada labarai na yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na PDP,

ADVERTISEMENT

Dele Momodu kan fejina 80 da Tinubu ya bayyana a matsayin manufofinsa a Abuja ranar Asabar a filin wasa na MKO Abiola.

Da yake mayar da martanin, Keyamo wanda ya kasance tsohon ministan samar da ayyuka yi ya ce tawagar kamfen din Atiku marasa amfani ne.

LABARAI MASU NASABA

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Ya ce ya yi tsammanin cewa Momodu zai yi cikakken bayani a tsakanin kundin mai dauke da shafuka 93 da Tinubu ya kaddamar da filin wasa na MKO Abiola.

Ya ce Atiku ya sace manufofi guda biyar na Buhari wanda ya cike a kundin yakin neman zabensa.

Ya ce daga cikin manufofin akwai fitar da miliyoyin mutane daga kangin talauci da sake farfado da wutar lantarki wajen bunkasa tattalin arziki, wanda kamata ya yi ya kirkiri nasa sababbin manufofin ba wai ya tsaya satar na Shugaba Buhari ba.

Keyamo ya ci gaba da bayyana cewa Momodu bai da abun da zai iya sukar Tinubu, domin ya yi kokarin kawo  nasa manufofin ba tare da ya sata dagawurin wani ba.

Zan Fallasa Badakalar APC – Atiku

Dan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya bayyana cewa zai fallasa dukkan badakalar da jam’iyyar APC ta yi lokacin da take rike da madafun iko bayan ya samu nasarar zama shugaban kasa.

Atiku ya bayyana haka ne lokacin da yake yi wa magoya bayansa jawabi a ranar Lahadin da ta gabata, ya siffanta babban zaben 2023 a matsayin raba gardama game da kwazon APC.

Ya kara da cewa jam’iyyar APC da kuma dan takarar shugaban kasarta, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu suna so su ci gaba da mulki duk da irin zagawa da suka yi, amma jam’iyyar PDP ba zata taba barin su ba.

Ya ce, “Lokacin da muka ziyarci Benin na bayyana manufofi na kararawajen gudunar da ayyuka da zai hade kanmu da ceto kasarmu Nijeriya.

“Shiri ne wanda ya kunshi dogon zango mai matukar kalubale a gare mu a halin yanzu, wanda dalilin da ya saya kin neman zabena ya karkata wajen tallafa su ga ‘yan Nijeriya kenan.

“A bangarena da kuma duk wanda yake a cikin jam’iyyar PDP, babban zaben 2023 shi ne zakaran gwajin dafi da zai auna kwazon APC.

“Jam’iyya mai mulki na kokarin gudu daga rashin gwazon su wanda hasali ma suna mayar da hankali akan abubuwan da ba su ta’allaka da zaben ba. Amma mu ba za mu taba basu dama ba. Sai mun bankado duk irin tsula tsiyar da suka tabka mun bayyanawa ‘yan Nijeriya.

“Ko da yake hakan ba zai gamsar ba. Abin da ya fi muhimmanci shi ne, karmu sake maimaita kuskuren da muka yi a baya.

“Wannan ya sa muka hadu domin mu bayyana muku manufofin kowacce jam’iyyar siyasa domin yanke hukuncin da ya dace lokacin zabe.”

Atiku jaddada cewa a matsayinsa na dan takarar shugaban kasa a karkashin inuwar jam’iyyar PDP, zai mayar da hankali ga dukkan matsaloli da suka addabi kasar nan.

Sulhu Tsakanin Atiku Da Wike Ya Sha Ruwa

Daga karshe dai, sulhu a tsakanin gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Ezenwo Wike da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya sha ruwa.

Wike ya bayyana cewa ba zai yi wa jam’iyyar PDP yakin neman zabe ba saboda ba a tuntube shi ba lokacin da aka dauki mambobin kamfen a cikin jiharsa.

Ya kara da cewa hotonan Atiku da na shugaban jam’iyyar PDP, Sanata Iyorchia Ayu sun yi batan dabo a cikin jiharsa saboda ba su san yayi yakin neman zabe a mataki na tarayya a jam’iyyar.

Wike ya bayyana hakan ne a lokacin kaddamar da kwamitin kamfen din jam’iyyar PDP a Jihar Ribas wanda ya gudana a garin Fatakwal.

Ya ce dan takarar shugaban kasa a jam’iyyary a zabi makiya Jihar Ribas a cikin kwamitin yakin neman zabensa na 2023.

Gwamnan ya ce, “Wasu mutane suna tambaya na kan dalilan da suka sa ba a ganin hotunan dan takarar shugaban kasa da kuma na shugaban jam’iyyar. Na ce musu me ye suke magana a kai? Dan takarar shugaban kasa ya shiga jihata ya dauko mambobin kwamitin yakin neman zabensa ba tare da gudummuwar gwamnan jihar ba.

“Dan takarar shugaban kasa ya shiga Jihar Ribas ya dauko wadanda yake bukata ba tare da bayar da gudummuwar gwamna ba. Sun ce basa bukata na a yakin neman zabensu, kuma hakan na nuna cewa ba sabukatar mutanen Jihar Ribas ne a cikin kwamitin kamfen dinsu.”

Wike ya ce shi da sauran ‘ya’yan jam’iyyar a jihar za su yi kamfen ne kadai ga dan takarar gwamna da na sanata da sauran wasu mukamai, amma ban da na dan takarar shugaban kasa.

Ya ce, “Idan da suna bukatarmu a cikin yakin neman zabensu da sun tuntube mu. Idan yana tunanin muna da muhimmanci, to da ya zo wurinmu. Babu wanda ya isa ya jagoranci Jihar Ribas fiye da ni a matsayina na gwamnan jihar.”

Gwamnan ya kara da cewa kowacce karamar hukumar guda 23 da ke jihar tana da hanyoyin da take bi wajen hada mutanenta.

PDP
Leadership Hausa
+ postsBio
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

MASU ALAKA

Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin
Manyan Labarai

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Wadanne Dalilai Ne Suke Sabbaba Karin Karbuwar Sin Tsakanin Al’ummun Duniya?

Wadanne Dalilai Ne Suke Sabbaba Karin Karbuwar Sin Tsakanin Al’ummun Duniya?

July 23, 2026
Ƙasashen Yankin Sahel 3 Sun Nuna Sha’awar Karɓar Bakuncin Gasar AFCON Ta 2032

Ƙasashen Yankin Sahel 3 Sun Nuna Sha’awar Karɓar Bakuncin Gasar AFCON Ta 2032

July 23, 2026
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Shekaru Biyar Na Bunkasa Makamashi Da Ake Iya Sabuntawa  

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Shekaru Biyar Na Bunkasa Makamashi Da Ake Iya Sabuntawa  

July 23, 2026
Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

July 23, 2026
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 25 Da Daddale Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Sada Zumunta A Tsakanin Sin Da Rasha

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 25 Da Daddale Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Sada Zumunta A Tsakanin Sin Da Rasha

July 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio

July 23, 2026
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

July 23, 2026
Sarkin Katagum Ya Jagoranci Addu’ar Roƙon Ruwa A Azare

Sarkin Katagum Ya Jagoranci Addu’ar Roƙon Ruwa A Azare

July 23, 2026
Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

July 23, 2026
Cire Tallafi: Majalisar Nasarawa Za Ta Binciki Yadda Aka Karkatar Da Kayan Tallafin Jihar

Gwamnan Nasarawa Ya Sallami Kwamishinoni Shida Na Majalisar Zartarwar Jihar

July 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.