• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Philippines Ta Sake Tada Rikici a Tekun Kudancin Sin Don Cimma Moriyarta

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
Philippines

Rundunar tsaron teku ta kasar Sin ta gabatar da wani bidiyo a daren jiya Laraba, wanda ya nuna yadda jirgin ruwa mai lamba 3003 na kasar Philippines ya matsa kusa da jirgin rundunar tsaron tekun na kasar Sin mai lamba 3302 bisa rashin kwarewa, har suka yi karo da juna. A wannan rana kuma, jirgin ruwa na rundunar tsaron teku na Philippines da jirgin ruwa mai gudanar da harkokin gwamnatin kasar da jiragen ruwan aikin su da dama sun shiga yankin teku na tsibirin Huangyan na kasar Sin ba bisa doka ba.

 

An lura cewa, a ran 8 ga watan Nuwamban da ya gabata, shugaban Philippines Ferdinand Marcos ya sa hannu kan wasu dokoki da suka hada da “Dokar yankin teku” da “Dokar hanyoyin jirgin ruwa a teku”, wadanda suka shigar da yankunan Sin kamarsu tsibirin Huangyan da yawancin yankin tsibiran Nansha da yankunan teku dake kewayensu cikin yankunan kasarsa ba bisa doka ba, da zummar tabbatar da haramtaccen hukuncin da ya yanke kan tekun kudancin Sin. Ba a cika wata daya da sanya wadannan dokokin ba, bangaren Philippines ya sake kutsa kai cikin tekun kudancin Sin, kuma burinsa shi tabbatar da haramtattun dokokin da ya zartas.

  • Gwamnoni Sun Miƙa Ta’aziyya Ga Wadanda Wani Abu Ya Fashe Da Su A Mota A Zamfara
  • Afirka Ta Kudu Za Ta Fara Bai Wa ‘Yan Nijeriya Bizar Shekaru 5

Ban da wannan kuma, an lura cewa, a karshen watan Nuwamban da ya gabata, a karon farko Amurka ta amince da jibge wata rundunar sojinta a Philippines da aka kira da “Rundunar soja ta musamman na sashen tudun ruwa na Ren’ai Jiao”. Matakin da ya zuga Phlippines ta dauki matakai yadda take so a tekun don cimma moriyarta.

 

LABARAI MASU NASABA

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Sin tana tsayawa tsayin daka kan warware rikicin tekun kudancin kasar ta hanyar shawarwari, da ci gaba da kiyaye cikakken ikonta na mallakar yankunanta da tekunanta ba tare da tangarda ba. Amma Philippines ta rika tada rikice-rikice ba iyaka, sai dai, munafuncin dodo ne ya kan ci mai shi. Kasashen da ba ruwansu kan wannan batu, wadanda suke zuga ta, ba za su dakatar da kokarin kasar Sin na tabbatar da hakkinta ba ko kadan. (Amina Xu)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka
Daga Birnin Sin

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil
Daga Birnin Sin

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025
Next Post
UNESCO Ta Sanya Bikin Bazara Cikin Jerin Al’adun Gargajiya Da Ba Na Kayayyaki Ba Da Aka Yi Gado

UNESCO Ta Sanya Bikin Bazara Cikin Jerin Al’adun Gargajiya Da Ba Na Kayayyaki Ba Da Aka Yi Gado

LABARAI MASU NASABA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.